Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
Published: 18th, April 2025 GMT
Shugaban ofishin siyasa na Hamas Khalil al-Hayya ya sanar da cewa, kungiyar a shirye take ta shiga cikin tattaunawa don tabbatar da cimma cikakkiyar yarjejeniyar musayar fursunoni, da tsagaita bude wuta a Gaza, da janyewar Isra’ila daga yankin, da kuma kaddamar da yunkurin sake gina yankin.
A cikin wani jawabi da kungiyar ta fitar, al-Hayya ya bayyana cewa, kungiyar Hamas a shirye take ta sako dukkan fursunonin da ‘yan gwagwarmaya ke tsare da su domin samun adadin fursunonin Falasdinawa da aka amince da su a halin yanzu da ake tsare da su a gidajen yarin Isra’ila.
Ya jaddada cewa, dole ne irin wannan yarjejeniyar ta hada da dakatar da yakin gaba daya, da janyewar sojojin Isra’ila baki daya daga Gaza, da fara aikin sake gina yankin, da kuma kawo karshen killacewar da ake yi wa yankin.
Al-Hayya ya yi maraba da kalaman na baya-bayan nan da Adam Boehler, wakilin Amurka a karkashin Shugaba Donald Trump ya yi, wanda ya bayar da shawarar magance matsalolin fursunonin da yakin da ake yi.
Al-Hayya ya bayyana matsayar Boehler a matsayin shawara mai kyau kuma ta daidai da mahangar Hama,s sannan ya nanata shirin kungiyar na cimma cikakkiyar yarjejeniya a karkashin wadannan sharudda.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Iran da Saudiyya za su iya magance yawancin matsalolin yankin Gabas ta tsakiya
Shugaban kasar Iran Mas’ud Pezeshkian ya jaddada cewa: Iran da Saudiyya za su iya magance yawancin matsalolin yankin Gabas ta Tsakiya ta hanyar dogaro da karfinsu a hade ba tare da bukatar shiga tsakani daga kasashen waje ba.
Shugaban kasar Iran Mas’ud Pezeshkian ya tarbi ministan tsaron kasar Saudiyya Khalid bin Salman a yammacin jiya Alhamis, wanda ke ziyarar aiki a birnin Tehran fadar mulkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran dauke da wata babbar tawagarsa.
Shugaban na Iran ya jaddada cewa Iran ta kuduri aniyar karfafa alakar ‘yan uwantaka a tsakanin kasashen musulmi.
Pezeshkian ta kara da cewa: Saboda wata wasiyya ta hadin gwiwa, shugabannin kasashen musulmi za su iya ba da misali mai kyau na zaman tare da samun bunkasar wadata.
Shugaban na Iran ya ci gaba da cewa: Iran a shirye take ta fadada alakar ta da Saudiyya ta kowane fanni.