Masarautar Gumel ta ce za ta bayar da dukkan goyon baya da hadin kai da ake bukata domin ci gaban yankin kasuwancin da ba shida shinge na Maigatari a jihar Jigawa.

 

Mai Martaba Sarkin Gumel Alhaji Ahmad Mohammad Sani ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kwamitin Jiha mai kula da shiyyar fitar da kaya ko kasuwanci maras shinge na Maigatari a fadar sa.

 

Ya ce, nan ba da dadewa ba majalisar masarautar za ta shirya taro da hakiman Gundumomi da Unguwanni da Kauyuka domin fadakar da al’ummarsu kan gudunmawar da suke bukata domin samun nasarar wannan yankin.

 

Sarkin wanda ya samu wakilcin Dallatun Gumel, Alhaji Musa Ayuba ya ce aikin noman rani da asibitin kashi da cibiyar dialysis da gwamnatin Malam Umar Namadi ta kafa a Gumel ayyuka ne da ke yin tasiri kai tsaye ga rayuwar al’ummar yankin.

 

Tun da farko shugaban kwamitin kula da shiyyar fitar da kaya da babu haraji ko shinge na jiha kuma kwamishinan kasafin kudi da kididdiga Alhaji Babangida Umar Gantsa ya ce sun je fadar sarkin ne domin sanar da shi irin nasarorin da aka samu tare da neman hadin kan sa da addu’o’i na uba.

 

Gantsa, ya kara da cewa gwamnati ta kashe makudan kudade wajen samun Amincewa da Lasisi domin sanya Maigatari fa matsayin wata kasuwa ko yanki da za a yi cinikayya maras shinge ko haraji don bunkasar Jihar Jigawa da kasa baki daya.

 

Shima da yake nasa jawabin Hakimin Gumel Arewa, Alhaji Sani Abdullahi Babandi ya yi kira ga ‘yan kwamitin da su tuntubi hukumomin da abin ya shafa don gyara hanyar gwamnatin tarayya da ta hada Gumel zuwa Maigatari domin samun damar shiga yankin cikin kwanciyar hankali.

 

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Maigatari

এছাড়াও পড়ুন:

Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim

Sayyid Ammar Hakim shugaban jam’iyyar ‘ تيار الحكمة الوطني’ na kasar Iraki ya bayyana cewa kasar Iraki ce kasa ta farko wacce zata amfani da tattaunawa tsakanin Iran da kasar Amurka.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto sayyid hakim yana fadar haka a jiya, ya kuma kara da cewa kasashen Iran da Iraki suna da gangantaka da musulunci makobtaka da kuma al-adu masu yawa. Don haka a duk lokacinda Amurka suka kyautata tsakanin Iran da Amurka kasashen biyu suna iya bude kan iyakokinsu don mu’amala da juna ba tare da Amurka ta shiga tsakanin ba.

A wani waje a cikin jawabinsa Hakim ya amince da ruwan da gwamnatin kasar Amurka ta taka wajen kauda tsohuwar gwamnatin kama karya na sadam Husaini. Da kuma kawo tsarin democradiyya wanda ya bawa mutanen kasar Iraki sararawa daga musibun sadam Husain a kan mutanen kasar.

Ya kuma kammala da cewa ‘amminsa shahid Bakir Hakim’ ya taba fadar cewa akwai bukatar mutanen kasar Iran su tattaunawa tsakaninsu da kasar Amurka don tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya ta kudu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa
  • Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Yi Aiki Tare Don Daidaita Mummunan Yanayi A Yankin Manyan Tabkuna Na Afirka
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas