Rundunar sojin sama na Operation Hadin Kai ta yi nasarar aiwatar da wasu hare-hare ta sama guda biyu, inda ta auka wa maboyar ‘yan ta’adda a yankin Sambisa na jihar Borno da kuma Kudancin Tumbun.

 

A wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame ya fitar, ya ce harin farko ya afku ne da misalin karfe 5:30 na safe a Kollaram- sanannar tungar ‘yan tada kayar baya, a ranar 15 ga watan Afrilu, inda aka kawar da mayaka da dama tare da lalata muhimman ababen more rayuwarsu.

 

Farmaki na biyu kuwa ya biyo bayan da misalin karfe 3:55 na rana a garin Arra na Sambisa, bayan binciken sirri da bincike da aka gudanar a baya an gano tarin ‘yan ta’addan, kuma hotunan da aka gani a zahiri sun tabbatar da kasancewar su. An yi amfani da ingantattun alburusai, wanda ya haifar gagarumar nasara da kuma kawo cikas ga ayyukan kungiyar.

 

A cewar sanarwar, wadannan ayyuka na baya-bayan nan wani bangare ne na ci gaba da yakin da aka tsara domin lalata karfin ‘yan ta’adda, da ruguza tsarin shugabancinsu da kuma kawar da mafakarsu a fadin Nijeriya.

 

PR/Usman Sani.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: barno Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
  • Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwasta Gadar Mandafuma A Jihar Borno
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato