Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Published: 18th, April 2025 GMT
Masu wannan fahimta sun yi imanin cewa duk lokacin da mutum ya ji baya son wani abu to a wurinshi wannan abin ba mai kyau ba ne. Haka nan kuma duk lokacin da mutum ya ji cewa ga wani abu amma shi ne ya kwanta mashi, toh wannan abin shi ne mai kyau.
Babban misalin da wadannan masu ra’ayi suke jaddadawa da nanatawa a kullum shi ne cewa a lokacin da mutum ya yi tsammanin cewa wani abu na da kyau a ra’ayinshi, to idan ya je cikin wata al’ummar zai tarar da cewa wannan abin barna ko wani abin ki.
Da irin wannan nazari ne aka samar da mafi shaharan nazariyyar nan ta NIHILISM, wanda ya zo da wasu ‘yan sauye-suye. Fahimtar ta Nihilism ta ce, sam babu wata doka da za ta iya bambancewa tsakanin abu mai kyau da mara kyau. Don haka ta hanyar ra’ayi da mahangar mutum ne kawai zai iya bambancewa tsakanin mai kyau da marar kyau.
Masu fahimta irin ta Nihilism sun tafi a kan cewa, dabi’ar mutum da yanayin mu’amalarsa da mutane ne kadai za ta iya ayyana nagartacciyar rayuwa ya ke yi ko akasinta. sannan kuma zantukan yabo ko zagi daga makusantan mutum su ma za su iya fayyace irin rayuwar da ya ke yi, ma’ana, abubuwan da suke fadi a kan shi.
Kowanne mutum yana dauke da wasu nauyayen abubuwa na irin dabi’un da ya kamata ya nunawa makusantanshi. Misali da akwai hakkoki na dabi’a da su ka wajaba akan shi wadanda da su ne zai mu’amalanci iyayensa. Haka nan shugaba akwai dabi’o’in da su ya kamata ya mu’amalanci mutanen da ya ke shugabanta.
Bayan samuwar wannan fanni na Nihilism, wanda shi ma ya zo da gudummawarsa dangane da yadda mutum zai gabatar da nagartacciyar rayuwa, sai masanin falsafa Plato ya bulla da sabon nazari wanda kaitsaye ya ke kalubalantar tushen nazariyyar Nihilism din. nazarin na shi ne ya yi kaurin suna har a ke yi masa lakabi da PLATONISM.
Plato cewa ya yi bayani kan wata babbar hanya da mutum zai bi ya gudanar da nagartacciyar rayuwa, inda a takaice ya ce, ‘Mutum ya nemi ilmi’. Ya ci gaba da cewa, a dai dai lokacin da mutum ya samu ilmi ya fahimci me ake nufi da nagartacciyar rayuwa, lallai babu wani abu da zai hana shi bin wannan hanya.
Plato ya ce aikata alfasha da masha’a duk suna aukuwa ne saboda karancin ilmin mai aikata su. Idan mutum ya fahimci ga gaskiya, ita zai bi domin gudanar da nagartacciyar rayuwa.
An zargi wannan nazarin da cewa, ta ya ya mutanen da ke da mabanbantan fahimta za su iya yin ilmin da za su yi nagartacciyar rayuwa? Sai ya ci gaba da bayanin cewa mutum duk ilminsa ba zai iya gano yadda ya kamata ya yi rayuwa ta gari ba, har sai ya samu horo na musamman dangane da abin da ake nufi da abu mai kyau da mara kyau.
Mutumin kuma da bai da kwakwalwar da za ta iya fahimtar karatu sai ya rika koyi da wadanda su ke da ilmi da horon gudanar da rayuwa mai kyau.
Plato ya ce, lura da tarbiyyar yara tana da muhimmanci wurin basu horo da ilmi, wanda kuma hakan zai sa su samu halayen kwarai da dattako. Yana da kyau al’umma ta yi kokarin ganin cewa wadanda ke mulkarsu (shugabanni) mutane ne masana, masu halin dattako da natsuwa da zurfin ilmi.
Lokacin da nazariyyar Platonism ta bayyana ta zama tamkar kishiya ga Nihilism. Domin kai tsaye nazarin ya yi dirar mikiya ne akan Nihilism da ra’ayoyinsa. kuma wannan tunani na Platonism ya samu karbuwa dari bisa dari a falsafar addinai. Sai dai wasu ‘yan bambance-bambance da ba za a rasa ba, da kuma gyare-gyare.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nagartacciya Rayuwa lokacin da mutum ya
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta shirya taron horaswa gaa malamai daga dukkan kananan hukumomi 27 domin shirya su, su horar da maniyyata aikin hajjin 2025 na jihar.
Darakta Janar na hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan a yayin wani taron karawa juna sani na kwana daya ga sabbin masu wa’azin aikin hajjin na kananan hukumomi.
Ya ce masu gudanar da aikin, an zabo su ne daga kowace karamar hukuma 27 na jihar domin gudanar da aikin hajjin mai zuwa.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce su kuma masu gudanar da aikin za su horas da maniyyatan a cibiyoyin da aka kebe a kananan hukumominsu na jihar.
Ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin wayar da kan jami’an ayyukan da gwamnatin jihar ta dora masu aikin.
Ya ce an yi hakan ne domin a tabbatar da horar da alhazan jihar yadda ya kamata kan abubuwan da suka shafi aikin Hajji.
“An umurci masu gudanar da aikin Hajji su horar da mahajjata kan wajibai, rukunan da ka’idojin aikin Hajji a Saudiyya.”
Labbo, ya yi nuni da cewa, tarbiyyar alhazai yadda ya kamata, zai shiryar da su gudanar da aikin Hajji kamar yadda addinin Musulunci ya tanada da kuma zama jakadu nagari na jiha da kasa baki daya.
A cewarsa taron bitar zai baiwa maniyyatan damar sanin ayyukan hajjin da ya dace kuma karbabbe.
Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta nada masu gudanar da aikin a cikin kwamitoci daban-daban domin ganin an samu nasarar gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ci gaba da bayanin cewa, a matsayinsu na jagororin alhazai, dole ne su kasance kusa da mahajjata don samun taimako a Najeriya da Saudiyya idan bukatar hakan ta taso.
Yayin da yake tsokaci kan shirye-shiryen, DG ya lura cewa, hukumar ta riga ta tattara tare da mika fasfunan kasa da kasa na maniyyata aikin hajjin na zuwa tsarin biza.
Ya bayyana daukar nauyin malamai daga dukkanin kananan hukumomi 27 na jihar zuwa kasar Saudiyya a matsayin irinsa na farko da gwamnatin jihar ta jigawa ta yi.
Tun da farko, Daraktan wayar da kan jama’a da yada labarai na hukumar Alhaji Abdullahi Aliyu ya yi wa jami’an jawabi a kan ayyukan da suka rataya a wuyansu a lokacin gudanar da aikin hajjin 2025.
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun yabawa Gwamna Umar Namadi da Darakta Janar na hukumar Ahmed Umar Labbo bisa amincewa da su na kasancewa cikin jami’an da za su jagoranci alhazan jihar domin gudanar da aikin hajjin nan gaba.
Sun kuma yi kira ga maniyyatan da su ba su hadin kai domin cimma burin da ake so.
USMAN MZ