Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano

Cibiyar Nazarin Dimokuradiyya ta Aminu Kano a Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta shirya taron shekara-shekara karo na 23 don tunawa da cika shekaru 42 da rasuwar Malam Aminu Kano.

 

 

A nasa jawabin, Shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya jaddada muhimmancin taron shekara-shekara wajen kiyaye manufofin da Malam Aminu Kano ya tsaya a kai.

 

Farfesa Haruna Musa wanda mataimakin shugaban jami’ar kula da harkokin ilimi ya wakilta, ya bayyana cewa jerin laccoci an yi niyya ne don ba da damar fahimtar juna dangane da yanayin tarihi.

 

“A ci gaba da kokarin da jami’ar mu ke yi na karfafa al’adun dimokuradiyyar Najeriya, muna gayyatar manyan mutane duk shekara don gabatar da laccoci a gidan Mambayya kan batutuwan da suka shafi kasa baki daya.

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, ya bayyana Malam Aminu Kano a matsayin wani hamshakin mai neman sauyi na Afirka, kuma dan gwagwarmayar siyasa mai jajircewa, wanda rayuwarsa ke ci gaba da zaburar da al’umma.

 

 

Wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jaddada cewa taken taron ya dace saboda halin da kasar nan ke ciki.

 

A nasa jawabin, Farfesa Kabiru Isa Dandago ya gabatar da kasida mai taken “Siyasar Gyaran Haraji a Najeriya: Tsammani da Gaskiya.

 

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa taron tunawa da marigayin ya hada masana, masana siyasa, da shugabannin kungiyoyin farar hula, inda suka yi bita a kan rayuwar marigayi dan kishin kasa, malami, dan juyin juya hali.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu
  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Masu Jan Hankalin Xi Jinping” A Kasar Malaysia
  • An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur 
  • Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde