Duk da cewa Atiku ya dage yayin tattaunawar da ya yi da manema labarai bayan ziyarar cewa ganawar ba ta batun siyasa ba ne, amma jawabin El-Rufai ya nuna karara akwai siyasa a cikin ganawar.

Bayan ziyarar ‘yan adawa kwanaki kadan da na gwamnonin APC, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya isa gidan Buhari sa’o’i kadan bayan tawagar Atiku, wanda ya kara tsananta siyasa.

Ya kuma ba da tabbaci ga ra’ayin cewa shugabannin jam’iyyar APC sun damu da siyasar tsohon shugaban kasar.

Masu lura da al’amura siyasa sun bayyana cewa kalaman da Ganduje ya yi bayan ganawar, ya tabbatar da cewa APC na yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa Buhari ya kasance tare da jam’iyya mai mulki. Wannan matakin na zuwa ne yayin da kawancen ‘yan adawa ke samun karfi, musamman a yayin da ake zaman doya da manja tsakanin gwamnatin Tinubu da ‘yan arewa.

Idan za a iya tunawa a lokacin watan Ramadan, dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya kai ziyarar girmamawa ga Buhari da sauran shugabannin siyasar arewa a lokacin rangadin da ya kai yankin.

Mai sharhi kan harkokin siyasa, Shamsudeen Ibrahim ya bayyana ziyarar da kwamitin gudanarwa na APC da Ganduje ke jagoranta suka kai ga Buhari a matsayin tsoron rasa riko, tsoron rasa arewa, da tsoron rarrabuwar kawuna. Ba ziyarar ‘yan’uwantaka ba ne. Ziyarar neman tsira ne.

Mai sharhi kan harkokin jama’a, Dakta Saidu Dukawa, ya kara da cewa ziyarar ta zama wata manuniya ga jama’a cewa shirye-shiryen zaben 2027.

Dukawa, ya kasance babban malami a jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), ya ce, “A bayana, ana yin irin wannan ziyarar ga tsoffin shugabannin kasa da suka hada da Obasanjo da Jonathan don cimma manufofin siyasa, amma yanzu lamarin ya zama tarihi. “

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Siyasa Buhari Ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Ya yi bayanin cewa aikin hanyar mai nisan kilomita 700 da ya tashi daga Abuja ya wuce Kaduna ya nufi Zariya zuwa Kano zai yi matukar rage yawan aukuwar hatsari da cunkoson ababen hawa da zarar aka kammala shi.

“Muna da sashe na 1, 2, 3. Sashi na 1 yana Abuja da Neja, sashe na 3 kuma yana Kano, kuma sashen Kano da ke tsakanin Zariya zuwa Kano tuni Julius Berger ya kammala shi, don haka gaba daya titin, 350, shi ne kilomita 240 da Julius Berger ya kammala.

“Sauran kilomita 140 da 2, 240 ta 2 shi ne 480. 140 ta 2 shi ne 280. Amma shugaban kasa ba kawai kammala 280 din ne ba, ya ma kara kusan sama da kilomita 11 a rukunin aikin da ke Kano domin jan titin har zuwa filin sauka da tashin jirage na kasa da kasa ta Malam Aminu Kano. Kuma aikin na ci gaba da gudana a halin yanzu, tare da sauran dan kadan da ya rage a Jihar Kano.

“Shugaban kasa ya kuma bayar da umarnin a sanya turakun hasken wuta mai amfani da haske rana gaba daya. Kuma zuwa yau, shugaban kasa ya bayar da kwangilar karasa sashi na 1 da na 3 na aikin mai nisan kilomita 118 a kan kudi naira biliyan 252.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu
  • PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike
  • Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • ’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna
  • KADGIS Za Ta Yi Amfani Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna