Aminiya:
2025-04-19@17:10:41 GMT

Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP

Published: 19th, April 2025 GMT

Jam’iyyar adawa ta SDP buƙaci Shugaba Bola Tinubu da sauran shugabannin siyasa a Najeriya su dai shagala da batun zaɓen 2027, su mayar da hankalinsu wajen magance matsalar tsaro da ke ƙara mayar da ƙasar tamkar filin kisa.

SDP ta bayyana cewa kashe-kashe ɗaruruwan mutane da ke faruwa a faɗin ƙasar nan – Arewa da Kudu – musamman a makonnin da suka gabata, na da matuƙar tayar da hankali.

Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na SDP, Araba Rufus Aiyenigba, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a daren Juma’a, cewa abubuwan takaicin sun hada da da kisan mafarautan Jihar Kano a jihar Delta, baya ga ayyukan ’yan ta’adda da hare-haren da a ka yi wa mutane sama da 100 a sassan jihar Filato.

Ya ce gwamnatin da ke kan mulki a yau ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita da za ta dakatar da wannan zubar da jini da ke gudana, yayin da ƙasar nan ke saurin zama filin kisa.

Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo

“A wasu makonnin da suka gabata, an kai munanan hare-hare da kisan gilla da ƙona wasu maharba daga Jihar Kano a yankin Edo, a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa arewa daga wani farauta a yankin Neja Delta.

“Haka kuma, a makon da ya gabata, an kashe sama da mutane ɗari ta hanyar kisan gilla tare da ƙona gidaje da yawa a Filato!

“An kuma ruwaito cewa wata sabuwar ƙungiyar ta’addanci mai suna ‘Makmuda’ ta kashe mutane da yawa, wanda ya ƙara dagula al’amuran ƙasarmu,” in ji Aiyenigba.

Ya yi zargin cewa jami’an tsaron ƙasar nan suna ƙara kasala da rashin ƙarfi, yayin da gwamnatin da ke kan mulki ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita.

Ya ce, “Abin damuwa ne yadda duk waɗannan kashe-kashe da ɓarna ke faruwa ba tare da an yi wani abu ba.

“’Yan siyasa a bayyane yake cewa, sun fi damuwa ne kawai da batun zaɓen 2027 da ke tafe. Muna buƙatar yin aiki don tabbatar da tsaron masu zaɓe kuma mu mallaki ƙasa kafin ma a fara maganar zaɓe,” in ji shi.

Kakakin jam’iyyar SDP na ƙasa ya ce yanzu ne lokacin da Tinubu zai nuna ƙarfin hali da ƙarfin zuciya a matsayinsa na shugaba, ya kuma yi abin da ya dace don tabbatar da tsaron al’ummar Najeriya.

“A matsayinsa na shugaban ƙasa, wajibi ne ya tabbatar da tsaron ’yan ƙasa, kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada, cewa jin daɗin jama’a da tsaro su ne babban manufar gwamnati.”

Ya ci gaba da mika ta’aziyyar jam’iyyar bisa rashe-rashen da aka yi a sakamakon wadannan matsalolin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rashin Tsaro Siyasa Tsaro Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

Duk da cewa Atiku ya dage yayin tattaunawar da ya yi da manema labarai bayan ziyarar cewa ganawar ba ta batun siyasa ba ne, amma jawabin El-Rufai ya nuna karara akwai siyasa a cikin ganawar.

Bayan ziyarar ‘yan adawa kwanaki kadan da na gwamnonin APC, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya isa gidan Buhari sa’o’i kadan bayan tawagar Atiku, wanda ya kara tsananta siyasa. Ya kuma ba da tabbaci ga ra’ayin cewa shugabannin jam’iyyar APC sun damu da siyasar tsohon shugaban kasar.

Masu lura da al’amura siyasa sun bayyana cewa kalaman da Ganduje ya yi bayan ganawar, ya tabbatar da cewa APC na yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa Buhari ya kasance tare da jam’iyya mai mulki. Wannan matakin na zuwa ne yayin da kawancen ‘yan adawa ke samun karfi, musamman a yayin da ake zaman doya da manja tsakanin gwamnatin Tinubu da ‘yan arewa.

Idan za a iya tunawa a lokacin watan Ramadan, dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya kai ziyarar girmamawa ga Buhari da sauran shugabannin siyasar arewa a lokacin rangadin da ya kai yankin.

Mai sharhi kan harkokin siyasa, Shamsudeen Ibrahim ya bayyana ziyarar da kwamitin gudanarwa na APC da Ganduje ke jagoranta suka kai ga Buhari a matsayin tsoron rasa riko, tsoron rasa arewa, da tsoron rarrabuwar kawuna. Ba ziyarar ‘yan’uwantaka ba ne. Ziyarar neman tsira ne.

Mai sharhi kan harkokin jama’a, Dakta Saidu Dukawa, ya kara da cewa ziyarar ta zama wata manuniya ga jama’a cewa shirye-shiryen zaben 2027.

Dukawa, ya kasance babban malami a jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), ya ce, “A bayana, ana yin irin wannan ziyarar ga tsoffin shugabannin kasa da suka hada da Obasanjo da Jonathan don cimma manufofin siyasa, amma yanzu lamarin ya zama tarihi. “

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike
  • Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa