Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka
Published: 19th, April 2025 GMT
Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman lafiya a Najeriya.
Da yake jawabi a wajen bikin nadin Alhaji Aliyu Dauda a matsayin Sardaunan Najeriya na farko, wanda aka gudanar a Yankari, Jihar Bauchi, Shugaban Kungiyar, Alhaji Ibrahim Haruna, ya bayyana gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen ci gaban kasa.
Alhaji Ibrahim Haruna ya ce, masarautun ba wai kawai suna zama uba ga al’umma ba ne, kawai har ila yau suna bada gagarumar gudunmawa wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.
Ya bayyana cewa goyon baya da gudunmawar da Alhaji Aliyu Dauda ke bayarwa ga masarautun gargajiya, musamman a Arewacin Najeriya, ne ya sa aka zabesa domin karbar wannan gagarumar karramawa.
A jawabinsa na karɓar nadin, Alhaji Aliyu Dauda ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta amince da gudunmuwar da Sarakuna ke badawa ta sanya su a cikin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.
Ya ce hakan zai ba da damar gudanar da aikinsu cikin ‘yanci ba tare da katsalandan ba.
Bikin ya samu halartar manyan baki, shugabannin al’umma da masoya daga sassa daban-daban na kasar, lamarin da ya zame wata babbar alama ta muhimmancin shugabancin gargajiya a Najeriya.
Rel: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gudunmuwa Kasa Kungiyar Lafiya Samarda Sarakuna Sarakunan Afirka
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Sakon jagora ga shugaban kasar Rasha yana da alaka da ci gaban kasa da kasa da na yanki
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana hakan ne a yau Alhamis a birnin Moscow na kasar Rasha cewa: Abu ne da ya dace a rubuta sakon da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya aikewa shugaban kasar Rasha dangane da ci gaban kasa da kasa da na yanki da kuma batutuwan da suka shafi kasashen biyu.
Araqchi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya isa filin tashi da saukar jiragen sama na Vnukovo da ke birnin Moscow a yau, yayin da yake amsa tambayar da wakilin IRNA ya yi masa kan abubuwan da ke cikin sakon jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei zuwa ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya kara da cewa: Ziyarar tasa tana da manufofi daban-daban, yana mai bayanin cewa, tun da farko an shirya ziyarar ne domin isar da rubutaccen sako daga Jagoran juyin juya halin Musulunci ga shugaban kasar Rasha, kuma ta zo daidai da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan da kuma tattaunawa ta kai tsaye.
Ya kara da cewa, tun a baya, har ya zuwa yanzu, a ko da yaushe Iran tana gudanar da shawarwari na kut-da-kut da abokanta na kasar Rasha kan batun makamashin nukiliya, yana mai cewa, suna kuma tattaunawa da Rasha da China, kuma a yanzu da aka samu damar da ta dace, za a iya yin shawarwari tare da jami’an Rasha.