Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
Published: 19th, April 2025 GMT
Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma sauran sassan jihar bisa nasarar kammala azumin Easter na kwanaki 40.
A madadin shugabanni da membobin majalisar ta 10, shugaban majalisar ya yaba wa mabiya addinin kirista saboda sadaukarwar da suka yi da kuma ci gaban ruhaniya a wannan lokaci mai tsarki.
Duk da haka ya yaba musu bisa sadaukarwar da suka yi a wannan lokacin kuma fatan sabunta ruhi da aka samu a lokacin Azumi ya kawo zaman lafiya, farin ciki, da wadata ga kowa.
Barr AbdulMalik Sarkin Daji, ya amince da muhimmiyar rawar da shugabannin addinin Kirista ke takawa wajen jagorantar al’ummar Nijar cewa majalisar ta 10 za ta ci gaba da samar da dokokin da za su kawo wa al’ummar jihar tasiri kai tsaye kuma mai kyau.
.
Hakazalika ya ce majalisar dokokin jihar Neja ta ci gaba da jajircewa wajen ganin an samar da zaman lafiya a tsakanin dukkan mazauna yankin, ba tare da la’akari da addini ko al’ada ba.
Bikin Ista, ginshiƙin bangaskiyar Kirista, tashin Yesu Almasihu daga matattu, alamar nasara akan mutuwa da zunubi, taron tunatarwa ne na ikon canza bangaskiya da saƙon bege mai ɗorewa wanda ke bayyana a tsawon shekaru.
PR ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka
Kungiyar Sarakunan Afirka ta jaddada muhimmancin gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen tabbatar da hadin kai da zaman lafiya a Najeriya.
Da yake jawabi a wajen bikin nadin Alhaji Aliyu Dauda a matsayin Sardaunan Najeriya na farko, wanda aka gudanar a Yankari, Jihar Bauchi, Shugaban Kungiyar, Alhaji Ibrahim Haruna, ya bayyana gudunmuwar da Sarakuna ke badawa wajen ci gaban kasa.
Alhaji Ibrahim Haruna ya ce, masarautun ba wai kawai suna zama uba ga al’umma ba ne, kawai har ila yau suna bada gagarumar gudunmawa wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.
Ya bayyana cewa goyon baya da gudunmawar da Alhaji Aliyu Dauda ke bayarwa ga masarautun gargajiya, musamman a Arewacin Najeriya, ne ya sa aka zabesa domin karbar wannan gagarumar karramawa.
A jawabinsa na karɓar nadin, Alhaji Aliyu Dauda ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta amince da gudunmuwar da Sarakuna ke badawa ta sanya su a cikin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.
Ya ce hakan zai ba da damar gudanar da aikinsu cikin ‘yanci ba tare da katsalandan ba.
Bikin ya samu halartar manyan baki, shugabannin al’umma da masoya daga sassa daban-daban na kasar, lamarin da ya zame wata babbar alama ta muhimmancin shugabancin gargajiya a Najeriya.
Rel: Adamu Yusuf