Aminiya:
2025-04-19@17:53:31 GMT

NAJERIYA A YAU: Sabbin dabarun hana matasa aikata laifi

Published: 19th, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Masu iya magana kan ce, banza ba ta kai zomo kasuwa.

Mai yiwuwa hakan ne ya sa matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka shiga ofishin ’yan sanda, su kuma fita ba tare da wani ya harare su ba, balle ya kama su.

’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da ƙwacen waya da fyaɗe kai har ma da satar mutane domin karɓar kuɗin fansa a tsakanin matasa.

NAJERIYA A YAU: Ainihin Abin Da Ke Hana Matan Arewa Koyon Ilimin Kimiyya DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo

Ko yaya wannan dabara take aiki?

Wannan ne abin da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye ta hanyar hadin gwiwa da inganta fasaha.

 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris ne ya bayar da wannan tabbacin a taron manema labarai na 2025 da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da ke Abuja ranar Alhamis.

 

Da yake jawabi bayan dawowar sa daga taron kungiyar masu yada labarai na duniya (NAB) a birnin Las Vegas na kasar Amurka, ministan ya ce taron mai taken “Fasahar, The Trend, The Future,” ya samar da wani dandali na yin cudanya da masu ruwa da tsaki a duniya kan sabbin abubuwa da suka tsara makomar watsa shirye-shirye.

 

Ya ce shigarsa wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Tinubu ke yi na bunkasa fasahar na bangaren yada labarai na Najeriya.

 

A cewarsa, “wannan zai tabbatar da kudurin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu sauyi mai dorewa a fagen yada labaran Najeriya.”

 

Ministan ya kuma bayyana irin rawar da ya taka a taron ‘yan kasuwan Najeriya da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa, inda ya gana da jami’an UNESCO kan shirin kafa cibiyar koyar da kafafen yada labarai da wayar da kan jama’a a Abuja. Ana sa ran Cibiyar da aka tsara za ta inganta tare da samarda ƙwararrun ‘yan jarida da haɓaka ayyukan watsa labarai masu dacewa.

 

Ya kuma kara jaddada cewa shirin gabatar da jawabai na ministocin da ake yi da kuma tarukan da aka shirya yi a fadin kasar nan na da nufin tabbatar da gaskiya, hada kan jama’a, da kara dankon zumunci tsakanin gwamnati da ‘yan kasa.

 

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, wanda ya bayyana muhimman ci gaban da aka samu a fannin samar da wutar lantarki, wanda ya yi daidai da ajandar gwamnati na bunkasa masana’antu a Najeriya da inganta samar da wutar lantarki a fadin kasar.

 

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya
  • ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
  • NAJERIYA A YAU: Ainihin Abin Da Ke Hana Matan Arewa Koyon Ilimin Kimiyya
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu