Aminiya:
2025-04-19@17:53:31 GMT

An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi

Published: 19th, April 2025 GMT

An shiga ruɗu da fargaba a garuruwan ƙasar Chadi da dama, sakamakon jita-jita da kafofin sada zumunta na yanar gizo ke yaɗawa cewa wasu matsafa na satar al’aurar maza.

Tun daga birnin Moundou da ke kudancin kasar da lamarin ya fara samun asali, inda wasu matasa hudu suka yi ikirarin cewa an sace musu al’aurarsu ta hanyar bakar tsafi, na yaduwa kamar wutar daji a wasu manyan biranen ƙasar Chadi.

Sakamakon jita-jita da bidiyoyi iri-iri da ake yadawa a shafukan sada zumunta, duk da cewa ba a tabbatar da wannan zargi a likitanci ko a hukumance ba, lamarin ya bazu tare da tada hankula har a tsakiyar N’Djamena, babban birnin kasar, inda wasu fusatattun mutane suka yi yunkurin kashe wani mutum wanda suka zarga da sace al’aurar wasu yara maza uku bayan ya yi musabaha da su, sai dai ya tsira da ransa sakamakon shiga tsakani da ’yan sanda suka yi, amma ya ji jiki da ɗan karen duka.

Babu tushe a zahiri

A yayin da ake fuskantar wannan al’amari wanda a halin yanzu girmansa na iya haifar da hargitsi na zaman lafiyar jama’a, gwamnati ta yanke shawarar tashi tsaye don ƙoƙarin kawo karshensa.

Kakakin gwamnatin Chadi, Gassim Cherrif ya ce lamarin na neman wuce gona da iri, domin kuwa ana kai wa mutane hari tare da jikkata da dama saboda zargi marasa tushe a zahari, yana mai cewa gwamnati ba za ta zuba ido tana gani har lamarin ya girma ba, ta yadda mutane ke ɗaukar doka da hannunsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Satar Al aura

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa

An tabbatar da mutuwar mutane bakwai a wani sabon harin da ‘yan ta’adda suka kai a kauyen Garaha Lar da ke jihar Adamawa. Shugaban karamar hukumar Hong, Honarabul Usman Wa’aganda ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa, wani mazaunin garin ya ɓata yayin da maharan suka lalata gidaje da kadarori. An Gudanar Da Harkokin Cudanya Da Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Malaysia A Birnin Kuala Lumpur  Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi Wa’aganda ya kuma bayyana cewa, wani Ɗan banga na yankin ya mutu bayan da wani bam ya tashi a lokacin da yake ƙoƙarin tabbatar da tsaron yankin. A cewarsa, motar ‘yansandan da ke sintiri ta ofishin ‘yansanda na Garaha ita ma ta ƙone yayin da wani abun  fashewa ya fashe acikin motar amma babu wani mutum da ya rasa ransa. Shugaban ya ce, tsoron bama-baman da maharan ke amfani da su ya sanya zuwa wuraren da aka kai hare-haren ke da matukar wuya. Wa’aganda ya buƙaci a tura sojoji yankin da kuma tallafa wa waɗanda harin ya rutsa da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • WAEC Ta Kwace Lasisin Makarantu 574 Sakamakon Satar Amsa
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • EFCC Ta Kama Wasu Mutane 40 Da Ake Zargi Da Yin Damfara Ta Intanet A Neja
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa