Tashar talbijin din “News Fox” ta kasar Amurka  mai ra’ayin ‘yan mazan jiya ta watsa wani rahoto da yake cewa; Daga lokacin da Donald Trump ya zama shugaban kasa, sau 6 sojojin Yemen su ka kakkabo jiragen sama maras matuki samfurin Mq9.

Rahoton na tashar talabijin din Fox ya kuma yi ishara da yadda sojojin na Yemen su ka kakkabo jirgin sama marasa matuki da marecen juma’a, wanda shi ne karo na 6 tun daga ranar 3 ga watan Maris.

Rahoton ya kuma kara da cewa; Kowane daya daga cikin jiragen sama marasa matuki  samfurin mq9 ya kai dalar Amurka miliyan 30.

 Bugu da kari rahoton ya kuma bayyana cewa; Sau 35 sojojin Amurka suna kai wa kasar Yemen hare-hare, amma kuma duk da haka har yanzu  sojojin Yemen suna ci gaba da kai wa wadannan jiragen na Amurka masu tsada hari. Haka nan kuma sojojin na Yemen suna ci gaba da hana wucewar jiragen  ruwa da suke zuwa HKI.

Wannan rahoton kuma ya yi ishara da yadda sojojin na Yemen suke kai wa HKI hare-hare da makamai masu linzami masu cin dogon zango. 

Daga fara kai farmakin Aksa zuwa yanzu, adadin jiragen Amurka samfurin  MQ 9 da sojojin yemen su ka kakkabo sun kai 16, sai dai wata majiyar ta bayyana cewa, jiragen da sojojin na Yemen su ka kakkabo sun kai 20. Wani jami’in ma’aikatar tsaro ta kasar Amurka ya sanar da tashar talbijin din ta Fox cewa; A 2024 Amurka ta kera, jragen MQ 9 guda 230, amma a kasar Yemen kadai an harbo 16 daga cikinsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen

Iran ta yi tir da Allah wadai da kakkausan lafazi da harin Amurka na baya baya nan kan tashar mai ta kasar Yemen, wanda ya yi sanadin mutuwar gomman mutane tare da lalata dukiya mai yawa.

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghai, ya kira harin da Amurka ta kai a matsayin keta kundin tsarin mulkin MDD da kuma dokokin kasa da kasa karara.

Misata Baghai ya ce : “Hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen, a matsayin cikakken goyon bayanta ga mamaya da kuma kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi a yankunan Falasdinawa, ya sanya Amurka ta zama mai hannu dumu-dumu a kan laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Falastinu da kuma yankin.”

Akalla mutane 80 ne suka rasa rayukansu tare da jikkata wasu 150 a harin da Amurka ta kai kan tashar jiragen ruwan ta Ras Issa a Yemen.

Wannan dai shi ne hari mafi muni tun bayan fara farmakin na Amurka a Yemen yau sama da watanni 15.

Sojojin Amurka sun sanar da cewa sun kai hari tare da lalata tashar jiragen ruwa na Ras Issa da ke lardin Hodeida a ranar Alhamis da nufin hana ‘yan Houthi kudaden shiga da suke amfani da su wajen daukar nauyin ayyukansu da kuma ta’addanci a yankin.

Saidai ‘yan Houtsis, sun ce ‘’Ras Issa “tashar ruwa ce ta farar hula inda jiragen ruwa da ke dauke da mai da dizal da iskar gas ke isa domin raba mai ga dukkan yankunan Yemen.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kaddamar Da Sabbin Hare-Hare Kan Garuruwan Sana’a, Sa’adah Da Al-Jawf Na Kasar Yemen
  • Dakarun Gwagwarmayar Yemen Sun Kai Hare-Haren Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?
  • Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka