Aminiya:
2025-04-19@22:52:00 GMT

Putin ya umarci tsagaita wuta a Ukraine albarkacin bikin Ista

Published: 20th, April 2025 GMT

Shugaba Vladimir Putin a yau Asabar ya umarci sojojin Rasha da su tsagaita buɗe wuta a Ukraine a wanan ranar ta Ista da kuma gobe Lahadi.

Putin ya kuma yi kira ga Kyiv da ta yi hakan, yayin da ake ganin tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura.

Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?

Haka kuma, Rasha da Ukraine sun yi musayar fursunonin yaƙi na sama da mutum 500 — kuma mafi girma tun bayan fara yaƙi a tsakanin kasashen biyu.

Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelenskiy, ya ce ƙasarsa ta karɓi sojoji fursunonin yaƙi akalla 277 waɗanda ke tsare a gidajen yarin Rasha, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Telegram.

Ita ma ma’aikatar tsaron Rasha ta ce ta karɓi sojojinta 246 daga Kiev, waɗanda a halin yanzu ke ƙasar Belarus wacce ke kawance da Rasha kafin daga bisani a maida su gida.

Kazalika, hukumomin Moscow da Kiev sun jinjina wa UAE wajen gudanar da wannan gagarumin aiki cikin kwanciyar hankali.

Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa dai ce ta shiga tsakani wajen ganin an yi musayar fursunonin cikin nasara tsakanin ƙasashen biyu da suka shafe shekaru uku suna gwabza yaƙi.

Bayanai sun ce Rasha ta kuma yi iƙirarin cewa ta kusan ƙwato yankunan da sojojin Ukraine suka mamaye tun lokacin bazarar shekara ta 2024 a yankin Kursk da ke kan iyakar Rasha.

Ƙasashen duniya na ci gaba da kira na ganin an kawo ƙarshen wannan yaƙi, duk da cewa Rashan da Ukraine kowanensu na iƙirarin samun galaba a yaƙin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Gombe, Bello Yahaya ya bayar da umarnin tura isassun jami’ai a fadin jihar domin samar da isasshen tsaro kafin bukin Easter, da kuma bayan bikin Easter.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar a Gombe.

 

A cewarsa, an tura jami’an dabarun dakile hare-hare zuwa muhimman wuraren da suka hada da wuraren ibada, wuraren shakatawa, kasuwanni, da sauran wuraren taruwar jama’a.

 

Ya kuma ce, kungiyoyin sintiri da jami’an tsaron cikin za su kasance a kasa domin sanya ido kan ayyukan da kuma gaggauta daukar matakin magance duk wata matsala idan ta taso.

 

Kwamishinan ya lura cewa rundunar tana aiki tare da hadin gwiwar ‘yan uwa jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma domin kula da su a cikin doka da oda yayin da ake ƙarfafa ‘yan ƙasa su kasance masu bin doka da oda kuma su kai rahoton duk wani abin da ake tuhuma ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

 

HUDU/GOMBE

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • An buɗe wa jami’an NDLEA wuta a Abuja
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista
  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha
  • Yawan Kudaden Da Al’ummun Sin Suka Kashe Kan Kayayyakin Masarufi Ya Kai Yuan Triliyan 12.5 A Rubu’in Farko
  • Babban Jami’in Diblomasiyyar Iran Ya Je Birnin Mosco Don Isar Da Sakon Imam Khaminae Ga Putin