Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Tattaunawa da Amurka an yi ta ne cikin yanayi mai inganci da hangen nesa

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana tattaunawar da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, wadda Oman ta shiga tsakani a birnin Roma na kasar Italiya, da cewa an gudanar da shi cikin yanayi mai ma’ana da hangen nesa.

A cikin wata sanarwa bayan tattaunawar, Araqchi ya yi nazari kan yanayin tattaunawar, inda ya bayyana cewa: “Sun gudanar da shawarwari na tsawon sa’o’i hudu a ci gaba da zaman da aka yi a baya, kuma sun samu kyakkyawar fahimta kan ka’idoji da manufofi da dama.”

Ya ci gaba da cewa: An amince da a ci gaba da tattaunawa, da shiga matakai na gaba, da fara taron kwararru. An shirya gudanar da tattaunawar fasaha a matakin kwararru a masarautar Oman daga ranar Larabar wannan makon.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  

Kasashen Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu domin cin moriyar juna a matsayinsu na makobta.

Wannan bayyanin ya fito bayan tattaunawa data wakana tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen biyu a birnin Yamai bayan kwashe watanni ana takaddama.

Yayin ziyarar da ministan harkokin wajen Najeriya ya kai Nijar an gudanar da wani babban taro tsakanin shugabannin diflomasiyyar kasashen biyu don sake farfado da hanyoyin hadin gwiwa a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki da tsaro.

Ministan harkokin waje da hadin gwiwa na  Nijar Bakary Yaou Sangaré da takwaransa na Najeriya Yusuf Maitama Tuggar sun gana a ranar 16 ga ga watan nan, lamarin dake nuni da wani gagarumin sauyi na dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu da ta yi tsami tsawon watanni biyo bayan juyin mulkin da ya faru a ranar 26 ga watan Yulin 2023.

bangarorin biyu sun kuma tattauna kan barazanar ta’addanci a kan iyakokinsu, inda suka jaddada aniyarsu ta hada karfi da karfe wajen yakar kungiyoyin da ke dauke da makamai da ke kawo cikas wajen aiwatar da dukkanin shirye-shiryen ci gaba a kasashen biyu cikin shekaru da dama. Inda suka bukaci ma’aikatun tsaron kasashen biyu da su ci gaba da hadin gwiwa a fannin tsaro.

Dangantaka tsakanin kasashen biyu da ke makwabtaka da juna ta tabarbare ne a lokacin da Najeriya ta taka muhimmiyar rawa wajen daukar matakan kakabawa Yamai takunkumin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS ta kakabawa kasar, wanda hakan ya bata dangantakar da ke tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Bayyana Cikakken Ikon Tawagar Masu Tattaunawan Iran A Zaman Shawarwari Da Amurka
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
  • Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Iran Tana Daukan Tattaunawarta Da Amurka Da Muhimmanci Don Neman Warware Takaddamar Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Wata Cibiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Bukaci Kama Jami’in Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Kasar Birtaniya