Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Zasu Ziyarci PTAD Don Neman Biyan Haƙƙoƙi
Published: 20th, April 2025 GMT
Shugaban Ƙungiyar Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Alhaji Ibrahim Ahmad Jikamshi, zai jagoranci wata tawaga ta musamman domin ganawa da Babban Sakataren Hukumar PTAD kan muhimman batutuwa fansho da ta shafi tsofaffin ma’aikatan.
Alhaji Ibrahim Jikamshi dayake bayani a Kaduna, yace za a gudanar da wannan ganawa a cikin wannan mako domin tattaunawa kan wasu matsaloli da aka gano wajen biyan bashin da ake bin tsofaffin ma’aikatan shekaru da dama.
Ya tabbatar da cewa ƙungiyar tana ƙoƙari wajen shawo kan irin waɗannan matsaloli da suka dade ana fama da su, tare da fatan cewa hukumar PTAD za ta nuna gaskiya, rikon amana da kuma jajircewa wajen biyan hakkokin da suka rage.
Alhaji Ibrahim Jikamshi, wanda ya tunatar da matakin da shugaban ƙasa ya ɗauka a baya na biyan bashin da ake bin tsofaffin ma’aikata ta hanyar sakin biliyoyin Naira, ya nuna damuwa da cewa har yanzu wannan mataki bai haifar da gamsasshen sakamako ba ga waɗanda abin ya shafa.
SULEIMAN KAURA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagar CPPCC Ta Ziyarci Nijeriya Da Cote d’Ivoire Da Senegal
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp