Ya kuma ce, kasar Sin tana adawa da duk wani nau’i na yakin karin haraji ko yakin kasuwanci. Kuma wannan ba wai don kare muradu da martabar kasar Sin ba ce kawai, har ma da kare tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa, tare da tabbatar da daidaito da adalci.

 

A cewarsa, “Idan har wata kasa ta dage kan kakaba mana yakin haraji ko kuma yakin kasuwanci, to tabbas za mu yi gaba-da-gaba da ita ba tare da tsoro ba, kuma tabbas za mu dauki kwararan matakan mayar da martani.

”(Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia

Rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe a ranar Alhamis ta tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali a unguwar Otobi da ke Ƙaramar hukumar Otukpo biyo bayan wani mummunan hari da ya tilastawa mazauna garin barin gidajensu.

Kakakin rundunar ’yan sandan, CSP Catherine Anene a wata tattaunawa ta wayar tarho da wakiliyarmu, ta kuma yi watsi da rahoton sabbin hare-haren da aka kai kan unguwannin Emichi, Okpomaju da Odudaje, inda ta bayyana su a matsayin rahoton ƙarya don yawo tsoratar da jama’a.

An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista

“Unguwar Otobi yanzu akwai kwanciyar hankali, mun bar wasu jami’anmu tun ranar Laraba ana gudanar da bincike,” in ji Anene.

A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia ya bayyana cewa har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyen ba bayan harin.

“Mun yi asarar mutane 11. Mun tura ƙarin jami’an tsaro,” in ji gwamnan yayin wani taron manema labarai inda ya bayyana hare-haren a matsayin batun ƙwace fili.”

Da yake mayar da martani kan wannan ci gaban, Sanata mai wakiltar mazaɓar Benuwe ta Kudu kuma shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Abba Moro ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta ci gaba da gazawa wajen kare rayuka, al’ummarsa za su iya amfani da hanyoyin kare kansu.

Sanatan, a cikin wata sanarwa da Emmanuel Eche’Ofun John, mashawarcinsa kan harkokin yaɗa labarai ya fitar, ya bayyana cewa hare-haren da suka janyo asarar rayuka da dukiyoyi na biliyoyin Naira abu ne da ba za a amince da su ba.

Ya kuma yi kira ga gwamnatoci a kowane mataki da su tashi tsaye wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kuma yabawa Gwamna Alia da a ƙarshe ya fito ya yi Allah-wadai da wannan aika-aika a jihar, ya kuma buƙace shi da ya ƙara yi wa al’umma aiki, yana mai jaddada cewa ƙoƙarin gwamnati a dukkan matakai bai isa ba.

Moro ya kuma yi kira da a kafa sansanonin hukumomin tsaro a cikin unguwannin jama’a masu rauni

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing
  • China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Duk Da Matsin Rayuwa: Bankuna Na Ci Gaba Da Cin Kazamar Riba Ta Hanyar Dora Wa Al’umma Haraji