Tsohon mashawarcin Shugaba Bola Tinubu kan harkokin siyasa, Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya lashe kujerar shugabancin Nijeriya a Zaɓen 2027 ba tare da goyon bayan yankin Arewacin ƙasar ba.

Hakeem Baba-Ahmed ya bayyana hakan a wata hira ta bidiyo tare da tsohon Babban Sakataren Hukumar Kula da Inshorar Lafiya (NHIS), Farfesa Usman Yusuf.

NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari?

Ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba yankin Arewacin Nijeriya zai fuskanci alƙiblarsa ta siyasa.

“Nan da watanni shida mutanen Arewacin Nijeriya za su fayyace inda suka dosa, saboda haka zaɓi ya rage wa mutanen sauran yankunan ƙasar.

“Sai dai abin da muka sani ƙarara shi ne babu wanda zai zama shugaban Nijeriya ba tare da goyon bayan Arewa ba.

Ya bayyana damuwa kan yanayin da aka tsinci kai a ƙasar a halin yanzu, inda ya buƙaci ’yan Arewa da su guji faɗa wa tarkon ’yan siyasa mayaudara a zaɓen da ke tafe.

“Muna so a samu gwamnatin da ta fahimci matsalolinmu kuma wadda za ta iya magance su.

“Bayan shekaru takwas da Buhari ya yi a karagar mulki mun ƙara buɗe ido. A yanzu wata gwamnatin ce amma har yanzu kuka muke yi. Shikenan kullum a kuka za mu ƙare?

Kazalika, Baba-Ahmed ya bayyana yadda yankin Arewa ya tagayyara a sakamakon rikicin Boko Haram wanda ya taɓa duk mabiya addinai, lamarin da ya jaddada muhimmancin haɗin kai.

“Mun dawo daga rakiyar yaudarar da ake yi mana ta zaɓen ɗan takara saboda ƙabilanci ko addini. Yanzu an rufe wannan babi.

“Yanzu abin da kawai muke buƙata shi ne shugaba nagari wanda zai magance matsalolin da muke fama da su,” in ji shi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Muhammadu Buhari Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere

 

A shekaru 70 da suka wuce, kasashen yamma sun yi wa taron Bandung kallon taro na kasashe matalauta, amma kuma ga irin yadda ya haifar da kyakkyawan sakamako ga mikewar kasashen. A zamanin yau, lokacin da kasar Amurka ke ta kara kakaba harajin kwastam a kan sauran kasashen duniya, muna farin cikin ganin yadda kasashe masu tasowa ke hada kansu, da rike tsaronsu da ci gabansu a hannunsu, suna kuma rungumar akidun zaman lafiya da hadin gwiwa da bude kofa don tinkarar yadda kasashe masu karfi ke neman cin zalin kasashe masu karamin karfi da ma rashin tabbas da ake fuskanta a duniya. Yau da muke waiwayen taron Bandung, za mu gano cewa, ko-ba-dade-ko-ba-jima za mu ga bayan nuna fin karfi a tarihin wayewar kan dan Adam. (Lubabatu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari?
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle