HausaTv:
2025-04-21@06:34:53 GMT

Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI

Published: 20th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da barazanar HKI na kaiwa cibiyoyin makamashin nukliyar kasar don hana kasar abinda take kira makaman Nukliya.

Ministan ya kara da cewa kasar Iran zata iya kare kanta ko da Amurka ce ta takaleta, kuma Amurka ta san hakan. Sannan ya ce HKI bata taba kaiwa Iran hari a bay aba kuma ba zata taba kai mata hari ba.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya buga wannan labarin a jiya Asabar ya kuma nakalto ministan yana cewa kasashen Rasha da Iran basu taba karfafa dangantakar tsakaninsu fiye da yanzu ba.

Aragchi ya kara da cewa kasashen Iran Rasha da kuma China suna aiki tare don tabbatar da zaman lafiya a duniya a cikin yan shekarun da suka gabata. Kuma kasashen da gaske suke a kan hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya

Gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan cewa zata rufe wasu daga cikin ofisoshin jakadancinta har kimani 30 a kasashen duniya, amma mafi yawansu a kasashen Afirka.

Shafin yanar gizo na labarai Afrika News ya nakalto ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurkan na fadar cewa gwamnatin shugaban Trump tana son ta rage yawan kashe kudade a ma’aikatar don amfani da su a cikin gida.

Labarin ya kara da cewa gwamnatin tana son rage kudaden da ma’aikatar take kashewa a kan ofisoshin jakadunsu da kasha 50% da kuma rage tallafin da take bawa wasu kungiyoyi a wadan nan kasashe har da kasha 75%.

Labarin ya kara da cewa kasashen da shirin ya shafa dai akwai  Lesotho, Eritrea, Afrika ta tsakiya, Congo Brazavile, Gambia, Sudan ta kudu,. Banda wadannan za’a rufe kananan ofisoshin jakadanci da ke birnin Durban na Afrika ta kudu, da kuma na Douala, da ke kasar Cameroon. Labarin yace ayyukan wadannan ofisoshin jakadanci zasu kuma ga kasashe makobta.

A kasahen turai da Asiya kuma Amurka zata rufe ofisoshin jakadancinta a tsibirin Malta, Luxembourg, da kuma wasu kananan ofisoshin jakadancin kasar a tarayyar Turai da Asiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta