Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Leicester City dake buga babbar gasar Firimiya ta kasar Ingila ta koma gasar yan dagaji ta Championship bayan da tayi rashin nasara a guda a wasanta da Liverpool.

Leicester wadda ta lashe gasar Firimiya a shekarar 2016 ta samu maki 18 kacal a wasanni 33 da ta buga, ta zura kwallaye 27 yayinda aka zura mata kwallaye 73 a ragarta, Leicester ta koma gasar Championship duk da cewar akwai sauran wasanni 5 da su ka rage ba a buga ba a gasar Firimiya ta bana.

Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila? Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya

Kocin Leicester Ruud Van Nistelrooy ya karbi ragamar horarwar Leicester a watan Janairu bayan raba gari da kungiyar ta yi da Steve Cooper, amma kuma abinda ake gujewa ya faru ga kungiyar wadda ke matsayi na 19 akan teburin gasar Firimiya.

Trent Alexander Arnold ne ya ci wa Liverpool kwallonta, wadda kuma ta kasance kwallo daya tilo a aka ci a wasan, zuwan Leicester gasar yan dagaji ya sa ta kasance kungiya ta biyu da ta koma bayan Southampton a bana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gasar Firimiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango

Bala’in Kogin Congo: Kwale-kwale ya kama wuta, ya kashe mutane 143

A wani mummunan lamari da ya afku a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, akalla mutane 143 ne suka mutu, wasu da dama kuma suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kama da wuta a kogin Kongo da ke arewa maso yammacin kasar.

Akalla mutane 143 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kama da wuta a kogin Kongo da ke arewa maso yammacin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, kamar yadda majiyoyin hukuma suka bayyana.

“An gano rukunin farko na gawarwakin mutane 131 a ranar Laraba, kuma an sake gano wasu 12 a ranakun Alhamis da Juma’a,” ‘yar majalisar wakilan kasar Josephine Pacific Lokomo ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

A nasa bangaren, Joseph Lokondo, shugaban kungiyoyin farar hula na yankin, ya bayar da bayanai kan adadin wadanda suka mutu na wucin gadi, wanda ya kai mutane 145.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • ’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun