Ana zargin wani ɗan kasar Indiya mai shekara 20 da tserewa da surukarsa mai shekara 40, kwanaki tara kacal kafin aurensa da ’yarta.
Ma’auratan Rahul da Shibani, matasa ne ’yan Aligarh, a Jihar Uttar Pradesh ta Indiya, wadanda suka shirya yin aure a ranar 16 ga Afrilu na watan da muke ciki.
Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa SaudiyyaAn aika wa dangi katin gayyata domin halartar taron bikin, amma kwanaki tara kafin ranar bikin, sai wani iftila’i ya afku.
Angon dan shekara 20 ya lallaba ya bace, amma bai tafi shi kadai ba; ya tsere da Anita, mahaifiyar amaryarsa mai shekara 40.
Domin munin lamarin, Angon da Anita sun kwashe kudaden ajiyar ma’auratan da kuma ajiyar dangin Anita, inda suka tatuke Shibani (amarya) da mahaifinta.
A ranar Lahadi 6 ga Afrilu, Rahul ya bar gidansu, yana mai cewa zai yi siyayya kayan biki.
Da daddare sai ya kira mahaifinsa ya shaida masa cewa, zai yi tafiya, amma kada ya damu da neman sa.
Kusan lokaci guda, Shibani ta lura cewa, mahaifiyarta da kudin ajiyarsu sun bace, sai dai ba ta bar wani sako ba.
Kodayake Shibani da mahaifinta mai suna Kumar sun lura da dangantakar da ba a saba ba gani ba a tsakanin Rahul da Anita, amma ba su ce komai ba, saboda ba sa son lalata auren.
“Ya kamata mu yi aure da Rahul a ranar 16 ga Afrilu, kuma mahaifiyata ta tafi tare da shi ranar Lahadi.
“Rahul da mahaifiyata sun kasance suna tattaunawa ta waya sosai a cikin wata uku zuwa huɗu,” kamar yadda Shibani ta shaida wa manema labarai na Indiya.
“Mahaifiyata ta kwashe duk kudinmu na shagalin bikin. Za ta iya yin dauk abin da take so yanzu, ba mu damu ba. Abin da muke so shi ne a mayar mana da kudinmu da kayan ado.”
Mijin Anita, Kumar yana sana’a ce a Bengaluru kuma yawanci ba ya zama, inda shi ma ya lura cewa Rahul ya fi yin magana da matarsa fiye da yadda yake yi da ‘yarsa.
Duk da haka, bai ce komai ba domin ranar biki ta kusa, kuma ba ya son bata abubuwa.
Ya shigar da karar wanda zai auri ’yarsa da matsarsa da suka bace da fatan ‘yan sanda za su iya gano su.
“Na kira Anita sau da yawa, amma ta kashe wayarta, na kuma kira mutumin da suke tare, amma ya ci gaba da musanta cewa ba ta tare da shi,” in ji Kumar.
Ya ce, “Wannan mutumin ba ya yin waya da ‘yata, said ai ya yi da matata,” in ji mahaifin Shibani.
“Ina zaune a Bengaluru don gudanar da kasuwancina, sai na ji cewa, tsawon wata uku da suka wuce, suna tattaunawa da juna na tsawon sa’o’i 22 a rana, na yi shakku, amma ban ce komai ba saboda an kusa daurin auren.
Anita ta tsare da mutumin a ranar 6 ga Afrilu kuma ta kwashe duk kudinmu da kayan ado.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen
Iran ta yi tir da Allah wadai da kakkausan lafazi da harin Amurka na baya baya nan kan tashar mai ta kasar Yemen, wanda ya yi sanadin mutuwar gomman mutane tare da lalata dukiya mai yawa.
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghai, ya kira harin da Amurka ta kai a matsayin keta kundin tsarin mulkin MDD da kuma dokokin kasa da kasa karara.
Misata Baghai ya ce : “Hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen, a matsayin cikakken goyon bayanta ga mamaya da kuma kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi a yankunan Falasdinawa, ya sanya Amurka ta zama mai hannu dumu-dumu a kan laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Falastinu da kuma yankin.”
Akalla mutane 80 ne suka rasa rayukansu tare da jikkata wasu 150 a harin da Amurka ta kai kan tashar jiragen ruwan ta Ras Issa a Yemen.
Wannan dai shi ne hari mafi muni tun bayan fara farmakin na Amurka a Yemen yau sama da watanni 15.
Sojojin Amurka sun sanar da cewa sun kai hari tare da lalata tashar jiragen ruwa na Ras Issa da ke lardin Hodeida a ranar Alhamis da nufin hana ‘yan Houthi kudaden shiga da suke amfani da su wajen daukar nauyin ayyukansu da kuma ta’addanci a yankin.
Saidai ‘yan Houtsis, sun ce ‘’Ras Issa “tashar ruwa ce ta farar hula inda jiragen ruwa da ke dauke da mai da dizal da iskar gas ke isa domin raba mai ga dukkan yankunan Yemen.”