Wasu Falasdinawa sun yi shahada a cikan kwana na 35 a sabon yakin da yahudawan sahayoniyya suka sake daurawa kan Zirin Gaza

Sojojin gwamatin mamayar Isra’ila suna ci gaba da yakin kisan kiyashi a Zirin Gaza tun bayan sake ci gaba da yau tsawon kwanaki 35 da suka gabata, bayan da Fira minista Benjamin Netanyahu ya yi watsi da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, kuma yana gudanar da wannan ta’asa ne tare da goyon bayan siyasa da na sojan Amurka, sannan kungiyoyin kasa da kasa gami da gwamnatocin kasashe sun daukin matakin yin shiru da rashin gwada wani yunkurin kalubalantar wannan danyen aiki.

Cibiyar yada labaran Falasdinu ta watsa rahoton cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-hare da dama tare da rusa gidaje, gami da karfafa haramcin shigar kayan abinci ga Falasdinawa tun farkon watan Maris da ya gabata. Wannan ya kara janyo bullar masifar yunwar da al’ummar Zirin Gaza ke fuskanta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI

Kungiyar Hamas wacce take iko da yankin Gaza, ta bada sanarwan cewa a shirye take ta saki fursina mai suna Edan Alexander wanda yake da jinsiyar Amurka da HKI don bude kofa ga tattaunawar tsagaaita wuta a gaza da kuma bude kofar rafa don samar da kayakin abicni a gaza.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jami’an kungiyar tana fadar haka a jiya Lahadi.

Khalil Al-Hayya shugaban kungiyar ya bayyana cewa Hamas ta amince da hakan ne bayan wata tattaunawa da Amurka kan batun. Ya kuma kara da cewa kungiyar tana son a fara tattaunawa da gaske tsakaninta da HKI ta hanyar masu shiga tsakani, don kawo karshen yakin da kuma ficewar sojojin yahudawa gaba daya daga Gaza. Da kuma bude kofar Rafa don shigowar kayakin agaji da abinci cikin yankin.

Khalil Al-Hayya ya kara da cewa hamas ta yadda a hada wata tawaga wacce zata gudanar da harkokin shugabanci a yankin.

A wani labarin kuma an tabbatar da cewa Falasdinawa kimani 109,000 ne suka yi shahada a zirin Gaza, tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023.

Binciken da aka guddanar ya nuna cewa sojojin yahudawna sun kashe falasdinawa akalla tsaknain 77,00-109.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Gaza
  • Sojojin HKI  Sun Sake Yin Kisan Kiyashi Mai Firgitarwa A Cikin Asibitin Gaza
  • Falasdinawa Sun Harba Wa HKI Makamai Masu Linzami
  • Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
  • Iran ta yi Allah wadai da harin da Isra’ila ta kai kan sansanonin ‘yan gudun hijirar Falasdinu
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Wani Sansanin Yan Gudun Hijira A Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Gudanar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Jabaliya Da Khan Yunus
  • Falasdinawa 1500 Ne Su Ka Zama Makafi Sanadiyyar Yaki
  • Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI