Ta ce, sakamakon dukan da ta sha, ta samu karaya a kafa da kuma raunin da ya shafi kunnenta.

 

Sai dai Shu’aibu ya musanta wannan ikirarin, inda ya tabbatar da cewa, an kama dan uwanta ne a yayin wani samame da aka gudanar a wurin wani shagali a birnin Katsina.

 

A cewarsa, an kama wanda ake zargin ne da laifin yin sojan gona da kuma yunkurin dakatar da jami’an Hisbah a lokacin da suke bakin aiki.

 

Da yake karin haske game da gaskiyar lamarin abinda ya faru, Shuaibu ya ce, an hana Hauwa shiga cikin ofishin Hisbah ne saboda irin tufafin da take sanye da su na rashin da’a, kuma ta yi yunkurin marin daya daga cikin jami’an Hisbah a lokacin da suka hana ta shiga.

 

Dangane da ikirarin da Hauwa ta yi na karaya a kafa, Shu’aibu ya ce hukumar ta bukaci iyalanta da su kawo mata shaidar na’urar haska kashi amma har zuwa lokacin taron manema labarai ba su samu wani takarda da ke tabbatar da raunin da ta samu ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ka Da Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano

An kuma buƙaci a ci gaba da siyasa cikin fahimta da girmama juna domin amfanin Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.
  • Ka Da Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 8 Kan Zargin Kashe Jariri A Borno
  • Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Rahoton Hana Shettima Shiga Villa
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
  • Minista Ya Sake Jaddada Ƙudirin Sabunta Kayan Aikin Watsa Labarai Na Gwamnati
  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno