Burnley Da Leeds United Sun Dawo Gasar Firimiya Lig
Published: 22nd, April 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Burnley United tare da takwararta ta Leeds United sun samu nasarar dawowa gasar Firimiya bayan samun nasara a mabanbantan wasannin da suka buga.
Burnley ta doke Sheffield United da ci 2-1 da yammacin yau domin samun wannan nasarar, hakazalika Leeds United ta samu nasara akan Stoke City da ci 6-0 a daya wasan na yau, dukkan kungiyoyin biyu zasu buga gasar Firimiya Lig ta badi.
Yayinda kungiyoyin Firimiya Southampton da Leicester City suka koma gasar Championship su kuma Burnley da Leeds United sun samu nasarar tsallakawa zuwa gasar Firimiya a kakar wasa ta badi.
Yanzu za a jira daya kungiyar daga Championship domin sanin wadanda zasu buga gasar Firimiya a badi, hakazalika za a jira kungiya daya da zata koma gasar yan dagaji daga Firimiyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Firimiya gasar Firimiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gharibabadi : inganta sinadarin uranium jan layi ne a tattaunawar Iran da Amurka
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta bayyana cewa tace uranium din ta tamakar jan layi ne a tattaunawar dake wakana tsakaninta da Amurka.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar ne Kazem Gharibabadi ya bayyana hakan, inda ya ce hakkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ne inganta sinadarin Uranium, yana mai jaddada cewa, wannan batu a matsayin jan layi a tattaunawar da Amurka.
Mista Gharibabadi ya bayyana haka ne a yayin taron kwamitin majalisar dokoki kan tsaron kasar da manufofin ketare, inda ya yi wa ‘yan majalisar bayani kan shawarwari zagaye na biyu tsakanin Tehran da Washington, wanda ya gudana a Rome, babban birnin kasar Italiya.
Jami’in na iran ya kara da cewa tawagar kasar ta jaddada matsayinta na cewa Iran ba ta neman kera makaman kare dangi, inda ya bayyana cewa ayyukan nukiliyar Iran na zaman lafiya ne gaba daya.
Mataimakin ministan harkokin wajen na Iran ya kuma jaddada cewa, daya daga cikin manyan makasudin shawarwarin shi ne cimma nasarar dage takunkumin da aka sanya wa iran gaba daya da suka hada da na majalisar dokokin Amurka da kuma umarnin zartarwar takunkuman matsin lamba da shugaba Donald Trump ya sanya wa hannu.
Kawo yanzu AMurka da Iran sun gudanar da shawarwari har guda biyu ka batun shirin nukiliyar kasar ta Iran, kuma dukkan bagarorin sun bayyana tattaunawar da mai kyakyawan fata.
A ranar Asabar mai zuwa bagarorin zasu sake ganawa a karo na uku, bayan wacce sukayi a Oman da kuma Italiya.