Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai
Published: 22nd, April 2025 GMT
A daren yau ne shugaba Bola Tinubu ya dawo Abuja bayan kammala ziyarar aiki ta makonni uku a Turai, inda ya gudanar da muhawara da manyan jami’an ƙasa da ƙasa don inganta dangantakar Najeriya a fannin tsaro da ci gaban tattalin arziki.
Jirgin shugaban ya sauka ne a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe a Abuja da misalin ƙarfe 9:50 na daren ranar, inda ya samu tarɓa daga manyan jami’an gwamnati, ciki har da Sakataren Gwamnatin tarayya, Sanata George Akume; Shugaban Ma’aikatan Shugaban ƙasa, Hon.
Shugaba Tinubu, wanda yayi tafiya tun a ranar Laraba, 2 ga Afrilu, ya fara ziyarar ne a Paris, Faransa, kafin daga bisani ya tafi Landan, Birtaniya.
Duk tsawon lokaci da yake wannan tafiya a Turai, shugaban ya ci gaba da tuntuɓar manyan jami’an gwamnati, yana bayar da umarnin aiwatar da muhimmancin al’amuran ƙasa, musamman ma na tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
Dubban jama’a ne suka hallara domin ɗaurin auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi a Fadar Mai Martaba Sarkin Bauchi ciki har da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima da Ministan Lafiya, Farfesa Mohammed Ali Pate, da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar.
Cikin baƙi akwai Shugaban Kamfanin rukuin Media trust Malam Kabiru Yusuf da sauran manyan baƙi suka hallara a birnin domin ɗaurin auren da kuma naɗin sarautar “Makama Babba I da aka yi wa tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Mohammed Abdullahi Abubakar.
Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a NejaAlhaji Bala Ahmad babban limamin Bauchi ne ya jagoranci ɗaurin auren, wanda Shettima ya kasance a matsayin waliyyin ɗiyar tsohon gwamnan yayin da Yusuf Yakubu Wanka, Chigarin Bauchi, ya kasance waliyyin angon, Sadiƙ Mohammed Wanka a wajen ɗaurin auren.
Bayan ɗaurin auren, Sarkin Bauchi, Alhaji Rilwanu Suleimanu Adamu ya naɗa wa tsohon gwamnan rawani a matsayin Makama Babba na farko, sannan ya sa baƙar Alkyabba.
Tun da farko mataimakin shugaban ƙasar, wanda ya sauka a filin jirgin sama na Sa Abubakar Tafawa Balewa ya samu tarba daga gwamnan jihar, Sanata Bala Mohammed da gwamnan Jihar Gombe Mohammed Inuwa Yahaya.
Haka kuma, taron ya samu halartar wasu manyan baƙi da dama, ciki har da tsohon gwamnan jihar Bauchi, Ahmadu Mu’azu, mataimakin gwamnan Yobe, Shugaban Kamfanin Media Trust Malam Kabiru Yusuf da sarakunan gargajiya da jama’a daga kowane fanni.
Fadar Sarkin dai ta cika maƙil a yayin da sauran manyan baƙi daga sassa daban daban su ma suka halarci bikin, inda aka ɗaura auren Sadiƙ Mohammed Wanka, da Khadijatu Mohammed Abdullahi Abubakar akan sadakin Naira 300,000.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya bayyana godiyarsa ga Shettima, Pate, Tuggar da Gwamnan Jihar Gombe da sauran manyan baƙi bisa halartar ɗaurin auren da kuma bikin naɗin sarautar tsohon Gwamna a matsayin Makama Babba na Bauchi na farko.
Ya kuma taya tsohon Gwamnan murna kan abin da ya bayyana a matsayin mafi kyawu kuma wanda ya cancanta saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar.