Kungiyar Hamas ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga Gaza da kuma kin amincewa da kisan kare dangi

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su tashi tsaye wajen gudanar da gangami da zanga-zanga a ranar Talata, domin nuna goyon baya ga Gaza, da tsayin dakanta, da kuma kawo karshen kisan kiyashi.

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, shugaban kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bukaci ‘yan Falasdinu gami da daliban jami’o’in Falasdinu masu ‘yanci a Yammacin Gabar Kogin Jordan da suke mamaye da su da su tashi tsaye tare da gudanar da zanga-zangar bacin rai da aka shirya za a fara a yau Talata, domin nuna goyon baya ga zirin Gaza da kuma yin watsi da yakin da ake yi na kawar da al’ummart yankin.

Jagora Shadid ya jaddada cewa, dole ne kungiyar dalibai a yammacin gabar kogin Jordan ta taka rawa wajen dakatar da kisan kiyashi da kuma daukar matakan gaggawa ga Gaza a dukkanin fagagen jama’a da jami’o’i, yayin da ake ci gaba da yakin kisan kiyashi da kuma fatattakar da ‘yan gwagwarmaya suke ci gaba da gwabza fada a fagen yakin ambaliyar al-Aqsa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A daidai lokacin da ake tunanin samun sauƙi daga tarin matsalolin tsaro da na tada ƙayar baya a Najeriya, sai ga wasu sabbin matsalolin na ƙara kunno kai.

Yayin da a wannan lokaci ake fuskantar hare-haren da ake zargin na ƙungiyar Boko Haram ne a Arewa maso Gabas, da kuma sabbin kashe-kashe a sassan jihohin Filato da Binuwai, sai kuma ga wata sabuwar ƙungiya da ake zargin ta ’yan ta’adda ce mai suna Mahmuda ta ɓulla a Jihar Kwara.

To ko mene ne ya haddasa wannan koma-baya ta fuskar tsaro?

Shin a ganinku, me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnatin” Najeriya?

NAJERIYA A YAU: Sabbin dabarun hana matasa aikata laifi DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan ƙara ƙazancewar matsalar tsaro da hanyoyin magance su a Najeriya.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
  • Kiristoci Sun Yi Zanga-zanga, Sun Nemi Adalci Kan Kisan Gilla
  • NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya?
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  • Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila