A yayin ziyarar, mataimakin shugaban kamfanin LEADERSHIP Mike Okpere, ya bayyanawa uwargidan shugaban kasa irin ayyukan agaji da Kamfanin LEADERSHIP ke gudanarwa tare da yin fatan hada hannu da shirin tallafin fata na gari ‘Renewed Hope Initiative (RHI)’ da nufin karfafawa mutane 1,000 da ayyukan yi.

 

A cewar Okpere, shirin zai mayar da hankali ne wajen samar da sana’o’in dogaro da kai a sassa daban-daban na tattalin arziki da suka hada da rini, kamun kifi, dinki da dai sauransu.

 

Ya yi nuni da cewa, manufar ita ce a taimaka wa daidaikun mutane su samu ‘yancin cin gashin kansu da kuma zama masu amfani a cikin al’umma.

 

Uwargidan shugaban kasar, wacce ta yi marhabin da shirin tallafin, ta kuma bai wa tawagar tabbacin yin hadin gwiwa da LEADERSHIP, musamman a fannonin da suka shafi karfafawa da kuma ci gaba mai dorewa.

 

Yayin da take nuna jin dadinta kan wannan ziyara da kuma irin goyon bayan da LEADERSHIP ke bayarwa a tsawon shekaru, Sanata Tinubu ta bayyana cewa, aikin taimakawa da tallafa wa ‘yan Nijeriya ba gwamnati ce kadai za ta iya yi ba, sai dai tare da hadin kan ‘yan Nijeriya baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin: Amurka Ta Buga Harajin Fito Kan Sassa Daban Daban Ba Tare Da Nuna Sanin Ya Kamata Ba

Daga nan sai Geng Shuang ya bayyana matsayar kasar Sin don gane da hakan, yana mai cewa, kasar na matukar jajantawa al’ummun Haitian bisa halin da suka shiga. Yana mai kira ga daukacin al’ummun duniya da su ci gaba da taimakawa kasar wajen karfafa tsare-tsarenta na ikon gina kai, da rungumar tafarkin neman ‘yancin kai, da dogaro da kai, da gaggauta hawa turbar neman ci gaba na kashin kai. Yayin da hakan ke wakana, Sin za ta ci gaba da taka rawar gani tare da dukkanin sassa masu ruwa da tsaki na kasar ta Haiti. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Amurka Ta Buga Harajin Fito Kan Sassa Daban Daban Ba Tare Da Nuna Sanin Ya Kamata Ba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • 2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
  • Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai
  • Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika
  • Shugaba Tinubu Zai Dawo Nijeriya A Yau Litinin Bayan Ziyarar Aiki A Turai
  • Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem