Guo Jiakun ya kara da cewa, kasar Sin ta kiyaye amfani da tsarin kimiyya da babu rufa-rufa a ciki mai baje komai a faifai, tare da nuna goyon baya da kuma shiga cikin kokarin da kasashen duniya ke yi na gano ainihin inda cutar ta samo asali.

 

Ya bukaci Amurka da ta daina siyasantar da lamarin, da amfani da batun gano asalin cutar a matsayin makami, kana ya nemi Washington ta guji yin kafar ungulu ga wasu kasashe, da dora wa wasu laifi, da yin watsi da tababar da ake ta nunawa a game da ayyukanta masu nasaba da cutar.

Kazalika, ya jaddada bukatar ganin Amurka ta warware matsalolin da kasashen duniya suka nuna damuwa a kai tare da bayar da cikakken gamsasshen bayani a kan lamarin ga al’ummar duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan

Kungiyar Hamas ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga Gaza da kuma kin amincewa da kisan kare dangi

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su tashi tsaye wajen gudanar da gangami da zanga-zanga a ranar Talata, domin nuna goyon baya ga Gaza, da tsayin dakanta, da kuma kawo karshen kisan kiyashi.

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, shugaban kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bukaci ‘yan Falasdinu gami da daliban jami’o’in Falasdinu masu ‘yanci a Yammacin Gabar Kogin Jordan da suke mamaye da su da su tashi tsaye tare da gudanar da zanga-zangar bacin rai da aka shirya za a fara a yau Talata, domin nuna goyon baya ga zirin Gaza da kuma yin watsi da yakin da ake yi na kawar da al’ummart yankin.

Jagora Shadid ya jaddada cewa, dole ne kungiyar dalibai a yammacin gabar kogin Jordan ta taka rawa wajen dakatar da kisan kiyashi da kuma daukar matakan gaggawa ga Gaza a dukkanin fagagen jama’a da jami’o’i, yayin da ake ci gaba da yakin kisan kiyashi da kuma fatattakar da ‘yan gwagwarmaya suke ci gaba da gwabza fada a fagen yakin ambaliyar al-Aqsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Yi Jana’izar Fafaroma Francis A Ranar Asabar A Vatican
  • Iran Ta Jaddada Matsayinta Kan Batun Tace Sinadarin Yuranium A Batun Tattaunawa Da Amurka
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • Sin: Matakin Harajin Kwastam Da Amurka Ta Dauka Babakere Ne 
  • Abubuwan da suka sa Fafaroma Francis ya yi fice a duniya
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar