Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi
Published: 23rd, April 2025 GMT
Gwamnatin Shugaban kasa John Mahama ta tsige Gertrude Torkornoo daga mukaminta na babbar mai shari’ar kasar, bisa wasu zarge-zarge da ake yi mata, domin bayar da damar gudanar da bincike.
Matakin da gwamnatin ta dauka na tsige babbar mai shari’ar ya jawo cece-kuce a tsakanin mutanen kasar.
Tsohon mai shigar da kara na kasar Godfrred Yeboah Dame ya yi tir da matakin na gwamnati da ya siffata da farmaki mafi girma akan ma’aikatar shari’a a tarihin kasar.
Ita kuwa jam’iyyar hamayya ta zargi shugaban kasa da tsoma baki a harkokin shari’ar kasar, domin nada alkalan da za su zama masu biyayya ga jam’iyyar da take Mulki ta ( NDC).
Torkornoo da ta hau mukamin nata a 2023, kuma ta kasance mace ta uku da ta rike wannan mukamin a tsawon tarihin ma’aikatar shari’ar kasar. Har ya zuwa yanzu dai ba ta ce komai ba akan tuhume-tuhumen da ake yi ma ta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sami Lambobin Yabo 8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
Kungiyar da take wakiltar Iran a wasannin Taekwondo na duniya a kasar Sin, ta sami lambobin yabo 8 a ranar farko da bude gasar ta kasa da kasa.
An fara wasannin na Tikondu a garin Tayan dake kasar China wanda shi ne karo na 7 da kuma ‘yan wasa 491 daga duniya suke gasa.
Daga cikin lambobin yabon din da tawagar ta Iran ta lashe da akwai gwala-gwalai 4, azurfa 3 da kuma tagulla.