Aminiya:
2025-04-23@21:30:40 GMT

Kawu Sumaila ya koma APC

Published: 23rd, April 2025 GMT

Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar Dattawa, Abdurrahman Kawu Sumaila ya tabbatar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.

Sumaila ya tabbatar wa Aminiya ficewarsa a wani saƙon kar ta kwana, bayan wallafa wa a shafinsa na Facebook.

Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC

“Gaskiya ne na koma APC.

Damuwata a ko yaushe ita ce walwalar al’ummar mazaɓata,” in ji shi.

Sanatan ya jaddada cewa matakin da ya ɗauka na sauya sheƙar ya yi shi ne domin inganta rayuwar al’ummar mazaɓarsa, da kuma tabbatar da ci gabansu mai dorewa.

Kawu dai ya daɗe da raba gari da tafiyar Kwankwasiyya da NNPP da ya yi takara ƙarƙashin ta, wanda ya sanya wasu da dama suka daɗe da hasashen zai sauya sheƙa zuwa tsohuwar jam’iyyarsa ta APC da ya bari a wancan lokacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kawu Sumaila Kwankwasiyya Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Rohoton Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Ya Tabbatar Da Tafka Manyan Laifukan Cin Zarafin Bil-Adama A Siriya

Wani rahoton kare hakkin bil adama ya tabbatar da aikata manyan laifuka a gabar tekun Siriya tare da yin kira da a kare fararen hula

Kwamitin da ke bin diddigin kare hakkin bil adama a kasar Siriya karkashin jagorancin dan gwagwarmaya Haitham Al-Manna, ya fitar da wani cikakken rahoton take hakkin dan Adam mai shafuka 72 da ke kunshe da jerin munanan laifukan da aka yi wa fararen hula a gabar tekun Siriya, yana mai bayyana shi a matsayin “neman shafe wata al’ummar daga kan doron kasa a kan tubalin sabanin Mazhaba”.

Rahoton wanda masu fafutuka 12 suka shirya, ya zo ne bayan kisan kiyashin da aka fara a ranar 6 ga Maris.

Rahoton ya yi nuni da wani tsari na cin zarafi da ake yi wa fararen hula, da suka hada da kashe-kashen gilla, azabtarwa, tilasta yin gudun hijira, da wawure dukiyoyi. Har ila yau, rahoton ya yi nuni da yadda dakarun gwamnati da kungiyoyin masu dauke da makamai suka shiga cikin wadannan laifuka, da kuma dogaro da shaidar iyalan wadanda abin ya shafa na tattara bayanan da aka hana binne mutane da kuma wulakanta fararen hula.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shawarar Tabbatar Da Tsaro A Duniya Ta Samar Da “Kyakkyawan Fata” Ga Duniya Mai Fama Da Tashin Hankali
  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC
  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 112
  • Rohoton Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Ya Tabbatar Da Tafka Manyan Laifukan Cin Zarafin Bil-Adama A Siriya
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Gwamna Zulum Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Titi Da Gadar Sama Ta Huɗu A Borno 
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tube a cikin daki