An Bayyana Filin Jirgin Sama Minna a Matsayin Mafita Ga Jiragen da ke sauka Abuja
Published: 24th, April 2025 GMT
A hukumance gwamnatin tarayya ta ayyana filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu dake Minna a matsayin mafita ga jiragen dake sauka Abuja.
Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan a yayin bikin kaddamar da jirgin saman na Overland Airways a filin jirgin sama na BAT dake Minna.
Festus Keyamo ya ce ana shirin daukar matakan da suka wajaba kamar su kwastam, shige da fice, ‘yan sanda, NDLEA da sauran su don sarrafa fasinjoji idan filin jirgin Abuja ya samu matsala.
Gwamnan jihar Neja Mohammed Umar Bago wanda ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa ci gaba da goyon bayan da yake baiwa jihar, ya bayyana cewa wannan nasara wani kokari ne na hadin kai na ganin an farfado da burin jihar a karkashin sabon tsarin mulkin gwamnatin sa.
A nasa bangaren, Wanda ya kafa kuma Manajan Darakta na Kamfanin Jiragen Sama na Overland, Kyaftin Edward Boyo ya bayyana cewa jirgin wani sabon salo ne da aka saya a matsayin sabon tsarin ci gaba tare da sabbin kayan fasahar zamani a bangaren zirga-zirgar jiragen sama yayin da ya ba da tabbacin samar da ayyuka masu inganci.
A nasa jawabin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris Malagi wanda ya yaba da ci gaban da gwamnan jihar Neja ya samu na tabbatar da manyan mafarkai ya kara yabawa ministan sufurin jiragen sama kan gagarumin ci gaba da aka samu a fannin.
Mohammed Idris ya jaddada cewa farashin kayan masarufi na raguwa sannu a hankali a kasar nan, biyo bayan dabarun da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dauka na tabbatar da samar da abinci a Najeriya, tare da ba da tabbacin samun kyakkyawar makoma ga ‘yan kasar.
ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: jiragen sama
এছাড়াও পড়ুন:
Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe
Hatsarin mota ya yi ajalin mutum biyar tare da jikkatar wasu takwas a yayin da suke bikin Ista a garin Billiri da ke Jihar Gombe.
Hatsarin ya faru ne a safiyar ranar Litinin, lokacin da direban wata babbar mota mai ɗauke da buhunan hatsi daga Jihar Adamawa ya auka kan dandazon jama’a da ke tsaka da shagalin bikin Ista.
An jingine wasanni a Italiya saboda mutuwar Fafaroma Francis An kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a BauchiA wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun yi gaggawar kai ɗauki, inda suka kwashe waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.
Sanarwar ta kuma ce bayan faruwar hatsarin, wasu fusatattun matasa sun cinna wa motar wuta tare da sace kayayyakin da ta ɗauko.
“Lokacin da ‘yan sanda suka kai ɗauki, matasan sun yi musu ruwan duwatsu, sai dai an shawo kan lamarin, kuma an dawo da zaman lafiya a yankin.”
Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Gombe, Bello Yahaya, ya bayyana jimami kan faruwar lamarin tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan.
Shi ma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayyana damuwa kan wannan iftila’i.
A cikin wata sanarwa da Babban Daraktan yada labarai na gidan gwamnati, Isma’ila Uba Misilli ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa lamarin abu ne mai girgiza zuciya.
Gwamnatin jihar ta yi alƙawarin ɗaukar nauyin magani ga waɗanda suka ji raunuka, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan kare faruwar irin wannan matsala a nan gaba.