Ma’aikatar yada labarai ta jihar Kano tare da hadin gwiwar hukumar kula da gidajen Radiyo da Talabijin ta kasa NBC sun shirya taron yini biyu ga masu fafutukar siyasa da masu sharhi kan harkokin yada labarai.

 

 

 

Taron na da nufin tsaftace harkar siyasa da inganta fahimtar juna tsakanin ‘yan siyasa a jihar.

 

An zabo mahalarta taron ne daga jam’iyyun siyasa daban-daban da gidajen rediyo a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

 

A nasa jawabin, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Waiya, ya bayyana cewa, a karshen taron, mahalarta taron za su fahimci ladubban da suka shafi harkokin siyasa.

 

Ya yi Allah wadai da karuwar kararrakin batanci da sunan siyasa, yana mai cewa masu fafutuka na siyasa, masu sharhi kan harkokin yada labarai da masu gabatar da shirye-shiryen siyasa na bukatar ilimin kan kyawawan ayyuka bisa al’adu da addini.

 

Kwamared Waiya ya nanata kudirin gwamnatin jihar na hada hannu da masu ruwa da tsaki domin ciyar da Kano gaba da kuma baiwa ‘yan kasa damar cin moriyar dimokradiyya.

 

“Ba mu zo nan don shawo kan kowa ya canza sheka zuwa wata jam’iyya ba amma don tsaftace tsarin”

 

Shima da yake nasa jawabin, kodinetan NBC na jihar Malam Adamu Salisu ya bayyana cewa taron bitar ya yi daidai da aikin hukumar, don haka akwai bukatar hada hannu da masu ruwa da tsaki domin cimma manufofin da ake bukata.

 

Ya yabawa ma’aikatar yada labarai kan wannan shiri, sannan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su bada gudunmawar ta hanyar samar da zaman lafiya.

 

Ya yi nuni da cewa taron ya yi daidai da aikin hukumar NBC.

 

Ko’odinetan jihar ya bayyana cewa masu fafutuka, masu sharhi kan harkokin yada labarai, da masu gabatar da shirye-shirye na da muhimmiyar rawa da za su taka a fagen siyasar Kano.

 

Da yake gabatar da kasida kan inganta magana mai kyau da kuma nisantar kalaman batanci a kafafen yada labarai ta mahangar Musulunci, babban limamin masallacin Al-furqan, Sheikh Bashir Aliyu Umar, ya bayyana wasu abubuwa guda uku na yada bayanai bisa koyarwar addinin Musulunci, wadanda suka hada da gaskiya, daidaito da kuma sanin yakamata.

 

Shugaban masu fafutukar siyasar jihar Kano, wanda aka fi sani da Gauta Club, Alhaji Hamius Danwawu Fagge, ya bayyana horon a matsayin wanda ya dace.

 

Ya yi alkawarin cewa mahalarta taron za su yi amfani da ilimin da aka samu wajen ci gaban Kano da Najeriya baki daya.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro yada labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da ya sa na bi sahun mahaifiyata a Kannywood — Maryam Intete

Maryam Abubakar, ɗaya ce daga cikin jaruman masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood ’yan ƙalilan da suka yi nasarar bin sahun iyayensu a harkar fim.

Matashiyar jarumar, wadda aka fi sanin ta da Maryam Intete a masana’antar, ta yi bayani a kan matsayinta na wadda iyayenta suka suka a cikin cikin harkar fim.

Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A wannan tattaunawar, jarumar ta yi bayani game da gogewarta da yadda ake samun daukaka a Kannywood, da wasu abubuwa game da ita kanta da iyayenta, da kuma sana’ar fim da dai sauransu.

Wace ce Maryam Abubakar?

An haife ni ne a Kano kuma a nan na girma. Na yi makarantar firamare da sakandare duk a Kano, daga baya na koma kasar Saudiyya inda na yi shekaru masu yawa a can.

Bayan na dawo Nijeriya ne na shiga harkar wasan fim kamar yadda na riski mahaifiyata na yi.

Ina da shekaru sama da ashirin, dangina na daga cikin masu shirya fina-finai a masana’antar Kannywood.

Idan mutum zai iya cewa sana’ar fim tana gudana a jininsa, to zan iya cewa fim na gudana a jinina, domin mahaifina ya dan yi aiki a masana’antar Kannywood kafin ya daina.

Mahaifiyata kuma har yandu tana ci gaba da taka rawa sosai a harkar shirya fina-finan Hausa.

Wanann ne ya sa na ce wasan kwaikwayo yana gudana a cikin jinina.

Amma duk da haka, ban taba tunani zama ’yar fim ba duk da cewa na kasance wani bangare na rayuwata a cikin harkar ta ginu.

Abin mamaki, bayan dawowata daga Saudiyya, na fara sha’awar bin sahun iyayena a sana’ar tasu.

Ko za ki iya mana karin bayani a kan su waye iyayenki da kika ce suna harkar fim?

Kamar yadda na faɗa a baya, mahaifina ya ɗan yi aiki a masan’antar amma mutane da yawa ba za su iya tunawa da shi ba ko da na ambaci sunansa.

Mahaifiyata kuma ta kasance ginshiki mai karfi a tarihin Kannywood, har yanzu tana taka rawa sosai a masana’antar domin tarihin masana’antar fina-finan Hausa ba zai cika ba sai an ambaci sunanta da kuma rawar da ta taka wajen ci gaban masana’antar.

Ba wata ba ce illa malama Hauwa Garba wadda aka fi sani da ’Yar Auta ko Sabura a cikin shirin Gidan Badamasi.

Ni ’yarta ce kuma ko ku yarda ko kar ku yarda nagartar mahaifiyata ce ta ja ni Kanywood.

Ana girmama ni saboda kasancewarta ’yarta kuma duk sauran ’yan wasan da na hadu da su a masana’antar a shirye suke su ba ni duk wata gudummawa da goyon baya da nake bukata.

Tun yaushe kike masana’antar Kannywood?

Yanzu dai na yi fiye da shekara biyu, kuma abin al’ajabi da sha’awa, shi ne, a cikin wannan ɗan gajeren lokaci, na yi fina-finai da yawa kuma na taka rawa a cikin kusan finafinai hudu.

Haka kuma, masu shirya fina-finai a kodayaushe suna son su saka ni a finafinansu musamman idan sun fahimci cewa ni ’yar Yar Auta ce.

Bayan fina-finan da na fito a ciki, ina da sauran fina-finan da ke jira na.

Dole ne in nuna godiya ta kwarai ga furodusoshin Kannywood bisa yadda suka amince da kuma yarda da iya wasana, dole kuma in yaba wa mahaifiyata saboda ta saukaka min tafiya, ta hanyar zama abin koyi ga yawancin matasa masu basira.

Yaya za ki kwatanta ranarki ta farko a gaban kyamara?

Ko da yake ba bakon abu ba ne a gare ni, amma bai kasance mai sauki kamar yadda nake tsammani zai kasance ba.

Idan za ka iya tunawa na gaya maka cewa na taso ne a cikin dangi inda wasan kwaikwayo ya bunkasa kuma don haka na san duk abubuwan da ke ciki.

Amma ba kamar yadda nake tunani ba, rana ta farko ta tabbatar mini da cewa akwai abubuwa da yawa fiye da abin da muke tsammanin harkar fim ta kunsa.

Abun burgewa shi ne kowa a shirye yake ya taimaka min kuma ya karfafa min gwiwa domin yin nasara.

Mene ne ra’ayin mahaifiyarki yayin da kika so shiga Kannywood?

Maganganun mahaifiyata su suke kara min karfin gwiwa wajen yin gaba kuma ina ganin tasirinsu a cikin tafiyata.

Ta ce da ni, “Maryam dole ne ki girmama kowa a wannan masana’antar, su ne manyanki kuma su ma za su yi miki jagora, ki tuna fa abokan aikin mahaifiyarki ne.”

“Wannan shi ne sirrina, ina mutunta kowa da kowa a masana’antar, kuma duk sun kasance kamar dangi ne a gare ni.

Za ki iya fitowa cikin fim daya tare da mahaifiyarki?

Fitowa a fim ɗaya tare da mahaifiyata abin alfahari ne gare ni, fim shi ne sana’ar da muke yi don dogaro da kanmu, mahaifiyata ta shahara a Kannywood kuma tana da dabi’u masu kyau, da suka cancanci a yi koyi da ita.

Kowa a masana’antar yana girmama ta saboda rawar da take takawa a duk shirin da aka saka ta.

Zan iya cewa fitowata a fim daya tare da ita zai zamo abin alfahari a matsayina na jaruma, dama ce a gare ni wacce ba kowa yake da ita ba.

Babbar nasara ce a gare ni shigowata cikin masana’antar Kannywood tun mahaifiyata tana taka rawar gani a cikinta.

Wanne abu ne ba za ki taɓa mantawa ba a matsayinki na jaruma?

Abin da ba zan taɓa mantawa ba a matsayina na jaruma shi ne duk lokacin da mutane suka nuna sun san ni a matsayin ’yar ’Yar Auta.

Girmamawa da kuma nuna sanayya da suke min a matsayin ’yarta abu ne da nake kauna wanda ba zan taba mantawa da shi ba a rayuwata.

Hakan ya nuna cewa mahaifiyata shahararriya ce, ta yi shuhura sosai a duniya, ta kafa kyakkyawan tarihi da hakan ke bin ’yayanta.

Kina da shirin da kike aikinsa a halin yandu?

Eh, ina aiki a kan shirin talabijin mai dogon zango mai suna ‘Baban Yawa’, kuma kamar yadda na faɗa a baya, ina da wasu ayyuka da ke jira na, amma a yanzu ina aiki a kan shirin mai dogon zango ne kawai.

Shin Maryam tana soyayya?

A gaskiya ba na yin soyayya. Babban abin da na sa a gaba shi ne na yi shuhura a cikin masana’antar, daga baya kuma sauran wasu abubuwa su biyo baya.

Za ki ci gaba da harkar Kannywood bayan kin yi aure?

A’a, ba na tunanin ci gaba, duk lokacin da na yi aure to na bar harkar fim a Kannywood ke nan.

Mece ce shawararki ga masu tasowa a Kannywood?

Su girmama kowa, ba da yawan fina-finai da ka fito ake samun ɗaukaka ba, shahara ita ce yawan mutane da kuka yi hulɗa da su ta hanyar wasan kwaikwayo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Siriya Tana Daukan Matakan Matsin Lamba Kan Gwagwarmaya Domin Samun Yardan ‘Yan Sahayoniyya
  • Iran za ta karbi bakuncin taron farko kan kare hakkin dan Adam a Gabas ta tsakiya
  • Tinubu ya gana da shugabannin tsaro a Abuja
  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC
  • Abin da ya sa na bi sahun mahaifiyata a Kannywood — Maryam Intete
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Ganduje Ya Soki Buba Galadima, Ya Ce “Ɗan Siyasa Ne Mara Tasiri”
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa