Sanarwar ta ƙara da cewa, ’yan kasuwa 1,000 za su samu jarin fara aiki na Naira 150,000 kowannensu, da nufin sauya akalar kasuwancin su zuwa sana’o’i na zamani a faɗin Jihar Zamfara.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa bayan hawansa mulki, gwamnatinsa ta bullo da shirye-shiryen ƙarfafawa da dama tare da samar da damarmaki don cimma manufofinsa na ceto.

 

“Waɗannan tsare-tsare ba wani kebantaccen abu ba ne, wani ɓangare ne na babban burinmu wajen samar da jihar Zamfara mai albarka don haɗa abokan hulɗa don magance ɗimbim matsalolin zamantakewa da tattalin arziki.

“Yawancin tsare-tsare na rage raɗaɗin talauci da wannan gwamnati ta bullo da su sun yi tasiri ga rayuwar dubban ‘yan jihar, ƙudirin gwamnatinmu na kawar da raɗaɗin talauci yana haifar da ɗa mai ido. Za mu ci gaba da yin haɗin gwiwa tare da UNDP da sauran ƙungiyoyin masu ba da tallafi don samar da ɗorewar hanyoyi don fitar da mutanenmu daga ƙangin talauci.

 

“Tun da aka fara wannan shirin na bayyana cewa akwai tsari wajen zabi na gaskiya na waɗanda za su ci gajiyar shirin, don haka an zabo waɗanda suka amfana daga garuruwa da ƙauyuka kamar Sankalawa, Furfuri, Karal, Gusau, da Bungudu.

 

“Ina yawan nanata cewa ƙarfafa tattalin arziki dole ne ya kasance cikin haɗin kai a ƙarƙashin mu, ba tare da barin al’umma a baya ba, shi ya sa na dage wajen ganin an rarraba damarmaki cikin adalci a dukkan ƙananan hukumomin.

 

“Hakazalika, an gudanar da shirye-shiryen horarwa ga duk waɗanda suka ci gajiyar noman rani. Mun yi imani da cewa samar da albarkatu ba tare da ilimin yadda za a yi amfani da su ba, zai iya iyakance tasirin da shirin ke son cimma.”

 

Gwamna Lawal ya kuma miƙa godiyarsa ga Hukumar Raya Ƙasashe ta Majalisar Ɗinkin Duniya kan yadda suka amince da manufofin gwamnatinsa na ci gaba. “Ga waɗanda suka ci gajiyar, ina ba ku umarni da ku yi amfani da waɗannan albarkatun bisa ga gaskiya, kar ku ba ni kunya a kan yardar da nake da ita akan ku.

“Da waɗannan kalamai, abin farin ciki ne na a hukumance na ƙaddamar da rabon kayayyakin noman rani ga masu cin gajiyar 300 tare da raba jarin fara aikin na N150,000.00 ga ‘yan kasuwa 1,000.”

 

Tun da farko, shugaban ofishin UNDP na Arewa maso Yammacin Nijeriya, Ashraf Usman, ya bayyana cewa tasiri, sha’awa, da azamar gwamnatin jihar Zamfara a bayyane yake ga kowa da kowa, wanda ke da matuƙar muhimmanci ga haɗin gwiwar.

 

“Na gode Mai girma Gwamna, waɗannan su ne dalilan da suka sa muka zo nan, ina taya ku murna da goyon bayan ɗimbin jama’a, na gode da irin misalin da ka ke bai wa sauran gwamnatocin jihohi wajen samar wa al’umma tallafi. Na gode da irin jagorancin ka.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe

Hukumar Ilimin Larabci da Musulunci ta Jihar Yobe (AISEB) ta fara rabon tabarmi da gidajen sauro ga almajirai a fadin jihar.

Sakataren Zartarwa na hukumar, Malam Umar Abubakar ya cen tabarmi da gidajen sauron tallafi na daga cikin kokarin da gwamnati ke yi na inganta walwala da rayuwar almajiran makarantun tsangaya a fadin jihar.

A cewarsa, shirin ya yi daidai da umarnin da gwamnatin jihar ta ba hukumar na tabbatar da kulawa da kuma tallafa wa yara almajirai.

Ya bayyana cewa an tsara rabon ga ɗalibai 100 a kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomin Jihar 17, wanda za a fara daga makarantun Goni Yahaya da Goni Muhammad Tsangaya da ke Damaturu.

Ya ƙara da cewa, kayayyakin za su taimaka wa almajirai su kasance da cikin tsafta da walwala, kuma hukumar za ta ƙara kaimi wajan samar da abubuwa kamar su ciyarwa, sutura, da samar da kayayyakin koyo da koyarwa.

A nasa jawabin godiya, shugaban makarantar Goni Muhammad Tsangaya Malam Goni Muhammad ya bayyana tallafi a matsayin wanda ya dace, kuma zai iya canza rayuwar almajiran, yana mai kira ga ƙungiyoyi da ɗaifaikun mutane da su yi koyi da irin wannan matakin.

“Hakan zai taimaka matuƙa wajen inganta rayuwar ɗalibanmu, musamman wajen hana kamuwa da cututtuka da sauro ke haifarwa da kuma samar da kwanciyar hankali yayin barci,” in ji shi.

Ana sa ran ci gaba da rabon kayayyakin nan da makonni masu zuwa a dukkan kananan hukumomin jihar 17.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
  • Wang Yi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu
  • Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya: Jigon Ziyarar Xi A Kudu Maso Gabashin Asiya
  • Motar hatsi ta kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe