Ministan Tsaron Pakistan Ya Yi Wa Pakistan Barazanar Kai Mata Hari Mai Tsanani
Published: 24th, April 2025 GMT
A daidai lokacin da sabani yake yin tsanani a tsakanin India da Pakistan, bayan wani hari da aka kai a Kashmir da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 26, ministan tsaron kasar Pakistan Khajah Asif ya ce; matukar India ta keta hurumin kasarsa, to kuwa za ta fuskanci mayar da martani mai tsanani.
Minista Khajah Asif ya kuma gargadi kasar ta India da ta guji keta hurumin kasar Pakistan.
Asif ya kuma bukaci India da ta gudanar da bincike akan harin da aka yi a ranar Talata a yankin Kashmir, kuma ta nesanci yin wani abu wanda zai jefa yankin cikin yakin da ba a san yadda karshensa zai kare ba. Haka nan kuma ya ce; Tushen matsalar tana nan a cikin kasar India,kuma wadanda su ka shirya kai harin suna nan a cikin India, don haka a cikin India ya kamata ta neme su.”
A lokaci daya kuma ministan tsaron na Pakistan ya jadada cewa; Kasarsa ba ta da sha’awar yaki ko kadan, amma idan aka kallafa mata yaki, to martanin da za ta mayar zai zama mafi dacewa kuma cikin karfi.”
A nashi gefen, ministan harkokin wajen kasar Pakistan Muhammad Ishaq Dar, ya ce, kasarsa tana sa ido da bibiyar abinda India take yi a kusa, kuma a shirye take ta kare tsaronta da iyakokinta.”
Dar ya kuma fada wa wata tashar talabijin din cewa; Pakistan kasa ce da take da makaman Nukiliya, tana kuma da dandazon makamai masu linzami masu karfi, kuma India ta kwana da sanin hakan, don haka ta guji keta hurumin kasar Pakistan da tsaronta.”
India ta zargi Pakistan da hannu a harin da aka kai a yankin Kashmir wanda ya yi sanadiyyar mutane 26. Kasar ta India ta kori Jakadan Pakistan daga kasarta, sannan kuma ta kira yi nata jakadan daga Islamabad. Bugu da kari Indiyan ta dakatar da aiki da yarjejeniya akan ruwa a tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Pakistan
এছাড়াও পড়ুন:
Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
Kafafen watsa labarun HKi sun amabci cewa daya daga cikin sojojinsu ya halaka a Gaza, yayin da wasu 7 su ka jikkata.
Kafafen watsa labarun na HKI sun ce, Harin da aka kai wa sojojin ya kunshi harbi daga kwararren maharbi da kuma harba makamin dake fasa motoci masu sulke.
An ga jiragen sojan mamaya suna tsananta hare-hare a yankin da lamarin ya faru, saboda su sami damar dauki gawar sojan nasu da kuma wadanda su ka jikkata.
Tashar talabijin ta 12; ta HKI ta ambaci cewa;Ana gwabza fada ne a arewacin Gaza, kuma mazauna yankin suna cewa sun ga jiragen sama masu yawa suna kai da komo.
Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare masu yawa a yankin Arewacin Gaza, kamar kuma yadda wata kafar ta ce an ji karar fashewar wasu abubuwa da karfi a cikin yankin Naqab ta yamma.
A wani labarin daga Gaza, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada a yau kadai sun kai 56.
Jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a yankunan Arewan yammacin Gaza da kuma Jabaliya da shi ne musabbabin shahadar adadi mai yaw ana Falasdinawan a yau.
A Jabaliya kadai jiragen yakin HKI sun kai hari ne akan wani gida da ‘yan hijira suke cikinsa, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 15.
A Arewacin Gaza kuwa mutane an sami shahidai 39, sai kuma wasu 7 da su ka jikkata a cikin birnin Gaza kamar yadda kamfanin dillancin labarun “Anatoli” ta Turkiya ya nakalto.