Kafafen watsa labarun HKi sun amabci cewa daya daga cikin sojojinsu ya halaka a Gaza, yayin da wasu 7 su ka jikkata.
Kafafen watsa labarun na HKI sun ce, Harin da aka kai wa sojojin ya kunshi harbi daga kwararren maharbi da kuma harba makamin dake fasa motoci masu sulke.
An ga jiragen sojan mamaya suna tsananta hare-hare a yankin da lamarin ya faru, saboda su sami damar dauki gawar sojan nasu da kuma wadanda su ka jikkata.
Tashar talabijin ta 12; ta HKI ta ambaci cewa;Ana gwabza fada ne a arewacin Gaza, kuma mazauna yankin suna cewa sun ga jiragen sama masu yawa suna kai da komo.
Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare masu yawa a yankin Arewacin Gaza, kamar kuma yadda wata kafar ta ce an ji karar fashewar wasu abubuwa da karfi a cikin yankin Naqab ta yamma.
A wani labarin daga Gaza, adadin Falasdinawan da su ka yi shahada a yau kadai sun kai 56.
Jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a yankunan Arewan yammacin Gaza da kuma Jabaliya da shi ne musabbabin shahadar adadi mai yaw ana Falasdinawan a yau.
A Jabaliya kadai jiragen yakin HKI sun kai hari ne akan wani gida da ‘yan hijira suke cikinsa, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 15.
A Arewacin Gaza kuwa mutane an sami shahidai 39, sai kuma wasu 7 da su ka jikkata a cikin birnin Gaza kamar yadda kamfanin dillancin labarun “Anatoli” ta Turkiya ya nakalto.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia
Ba wannan ne karon farko da ake zargin wasu ‘yan ƙasashen waje da kai hare-hare a Nijeriya ba.
A baya an yi zargin cewa ƙungiyoyi kamar Lakurawa da ke kai hare-hare a jihohin Sakkwato da Zamfara, sun samo asali ne daga ƙasashen waje.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp