Jagora: Tafarkin Imaman Ahlul Bayti ( A.S) Na Gwgawarmaya Ne Da Jajurcewa
Published: 24th, April 2025 GMT
Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah sayyid Ali Khamnei wanda ya gabatar da jawabi dangane da zagayowar ranar shahadar Imam Ja’afar Assadiq ( a.s) ya bayyana cewa: Tafarkin Imaman Ahlul-Bayti (a.s) ya kasance na gwgawarmaya da jajurcewa, kuma koyarwarsu ta ginu ne akan mandiki da kafa dalili.
Jagoran juyin musuluncin na Iran ya ce; rayuwar Imam Ja’afar Assadiq ( A.
Jagoran juyin musuluncin na Iran ya siffata mutanen Gaza da Lebanon da cewa suna tafiya ne akan wannan tafarki na Imaman shiriya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: China da Rasha abokan hulda ne na tushe ga Iran bisa kyakkyawan tsari
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana kasashen China da Rasha a matsayin abokan huldar na tsari a kan tubalin manyan tsare-tsare ga Iran, kuma ya dace kasashen uku su ci gaba da tuntubar juna a fannoni daban daban.
A yayin da ya isa birnin Beijing, yayin da yake amsa tambaya game da makasudin ziyararsa a kasar China a jajibirin shawarwarin da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, Araqchi ya bayyana cewa: Kasashen China da Rasha abokan hulda ne na kut-da-kut da Iran. Sun kasance tare da Iran a lokutan wahala, kuma abu ne mai kyau cewa Iran suna ci gaba da tuntubar juna tare da su a fagage daban-daban, musamman a yanzu da aka tabo batun tattaunawa da Amurka a fakaice.
Araqchi ya ci gaba da cewa: “Suna bukatar su sanar da abokansu da ke kasar China cikakkun bayanai game da abubuwan da ke faruwa tare da tuntubarsu, kuma sun yi hakan a makon da ya gabata a kasar Rasha.” Inda ahalin yanzu suke kasar China, kuma zai isar da sakon shugaba kasar Iran Mas’ud Pezeshkian, kuma idan Allah ya yarda za su yi tattaunawa mai kyau.