Baffa Bichi, Kabiru Rurum, Sha’aban Sharada Da Wasu Sun Koma Jam’iyyar APC
Published: 24th, April 2025 GMT
Tsoffin kwamishinoni na Jihar Kano kamar su Hon. Diggol, Hon. Abbas Sani da Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Baffa Bichi su ma sun koma APC.
Hakazalika, Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada wanda ya tsaya takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar ADP a zaɓen 2023, ya sauya sheƙa zuwa APC.
Ana kallon wannan sauya sheƙar a matsayin wani babban tagomashi ga jam’iyyar APC musamman a Jihar Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Sha aban Sharada Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
Ma’aikatar yada labarai ta jihar Kano tare da hadin gwiwar hukumar kula da gidajen Radiyo da Talabijin ta kasa NBC sun shirya taron yini biyu ga masu fafutukar siyasa da masu sharhi kan harkokin yada labarai.
Taron na da nufin tsaftace harkar siyasa da inganta fahimtar juna tsakanin ‘yan siyasa a jihar.
An zabo mahalarta taron ne daga jam’iyyun siyasa daban-daban da gidajen rediyo a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.
A nasa jawabin, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Waiya, ya bayyana cewa, a karshen taron, mahalarta taron za su fahimci ladubban da suka shafi harkokin siyasa.
Ya yi Allah wadai da karuwar kararrakin batanci da sunan siyasa, yana mai cewa masu fafutuka na siyasa, masu sharhi kan harkokin yada labarai da masu gabatar da shirye-shiryen siyasa na bukatar ilimin kan kyawawan ayyuka bisa al’adu da addini.
Kwamared Waiya ya nanata kudirin gwamnatin jihar na hada hannu da masu ruwa da tsaki domin ciyar da Kano gaba da kuma baiwa ‘yan kasa damar cin moriyar dimokradiyya.
“Ba mu zo nan don shawo kan kowa ya canza sheka zuwa wata jam’iyya ba amma don tsaftace tsarin”
Shima da yake nasa jawabin, kodinetan NBC na jihar Malam Adamu Salisu ya bayyana cewa taron bitar ya yi daidai da aikin hukumar, don haka akwai bukatar hada hannu da masu ruwa da tsaki domin cimma manufofin da ake bukata.
Ya yabawa ma’aikatar yada labarai kan wannan shiri, sannan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su bada gudunmawar ta hanyar samar da zaman lafiya.
Ya yi nuni da cewa taron ya yi daidai da aikin hukumar NBC.
Ko’odinetan jihar ya bayyana cewa masu fafutuka, masu sharhi kan harkokin yada labarai, da masu gabatar da shirye-shirye na da muhimmiyar rawa da za su taka a fagen siyasar Kano.
Da yake gabatar da kasida kan inganta magana mai kyau da kuma nisantar kalaman batanci a kafafen yada labarai ta mahangar Musulunci, babban limamin masallacin Al-furqan, Sheikh Bashir Aliyu Umar, ya bayyana wasu abubuwa guda uku na yada bayanai bisa koyarwar addinin Musulunci, wadanda suka hada da gaskiya, daidaito da kuma sanin yakamata.
Shugaban masu fafutukar siyasar jihar Kano, wanda aka fi sani da Gauta Club, Alhaji Hamius Danwawu Fagge, ya bayyana horon a matsayin wanda ya dace.
Ya yi alkawarin cewa mahalarta taron za su yi amfani da ilimin da aka samu wajen ci gaban Kano da Najeriya baki daya.
KHADIJAH ALIYU