HausaTv:
2025-04-25@12:00:10 GMT

MDD : ba tabbas kan ko za’a kawar da zazzabin malaria nan da shekarar 2030

Published: 25th, April 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa ba tabbas ko za’a iya kawar da cutar zazzabin cizon sauro nan da shekarar 2030, musamman a nahiyar Afrika.

Fiye da mutane miliyan 263 ne suka kamu da cutar a cikin 2023, kuma kusan 600,000 ne suka mutu sanadin cutar a cewar alkalumman na MDD.

Musamman a wannan lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya rage kashe kudaden tallafi na kasa da kasa, inji rahoton.

A cikin shekaru 25, zuba jari a yakin da ake yi da zazzabin cizon sauro ya hana kamuwa da cutar ga mutane biliyan 2 da kuma mutuwar mutane miliyan 13, musamman a Afirka.

“Akwai babbar barazana, da kuma bukatar jajircewa wajen samar da magunguna in ji Philippe Duneton, darektan Unitaid, kungiyar da ke da fafatuklar samar da magunguna na HIV, tarin fuka ko TB da kuma zazzabin cizon sauro.

Bayyanin ya fito ne gabanin zagayowar ranar duniya ta yaki da cutar zazzabin sauro yau 25 ga watan Afrilu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya

Ban da haka, yadda gwamnatin Trump ba ta da tabbas a kan manufofinta na haraji yana kuma ba kasashen duniya mamaki. Ba a jima ba da gwamnatin Amurka ta sanar da matakinta na harajin ramuwar gayya a kan kasashen da ke ciniki da ita, sai kuma ga shugaba Trump ya sanar da dage harajin a kan wasu kasashe na kwanaki 90. Kuma kashegari sai aka ji ya yi barazanar cewa, in dai ba a kai ga cimma daidaito a shawarwari ba, to, Amurka za ta maido da harajin. Ban da haka, gwamnatin Amurka ta kuma yi gyara ta ba-zata a kan dokokinta na haraji, inda ta cire harajin ramuwar gayya a kan kayayyakin lataroni da suka hada da wayar salula da kamfuta da sauransu.

 

Haraji abu ne da ya shafi manufar kasa, amma ga shi gwamnatin Amurka ta mai da shi kamar wasa, wanda hakan ya bayyana rashin tunani na manufofin haraji na kasar, da ma yadda take mai da su a matsayin makamai na nuna fin karfi a duniya. Amurka ta ce wai tana neman tabbatar da yi mata adalci ne, amma a hakika kuwa, tana neman kakaba fifikonta ne a kan sauran kasashe.

 

Tabbatar da ci gaba hakki ne ga kowace kasa a maimakon wasu kasashe kalilan. Kasashen duniya na rungumar adalci a maimakon nuna fin karfi. Tabbas Amurka za ta cije a yunkurinta na neman tabbatar da fifikonta a kan sauran kasashen duniya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
  • Sama Da Mutane Miliyan 11 Ne Ke Fama Da Ciwon Suga A Najeriya – Farfesa Zubairu Ilyasu
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Siyasantar Da Batun Asalin Cutar COVID-19 
  • 2024: Manyan Alkaluman Sufuri 2 Na Filayen Jiragen Sama Na Kasar Sin Sun Kafa Tarihi