Aminiya:
2025-04-25@11:24:11 GMT

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa 

Published: 25th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wani sabon ango, sun kuma yi wani gaba da amaryasa bayan kwanaki 11 da ɗaura aurensu a wata unguwa a Jihar Nasarawa.

Ganau sun shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun kai hari gidan sabbin ma’auratan ne da misalin ƙarfe karfe 11:00 na dare ranar Laraba, inda suka harbe angon har lahira, sannan suka tafi da matar zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Name(required) Email(required) Website Message

Submit

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Akaleku, da ke Ƙaramar Hukumar Obi ta Jihar Nasarawa, a kan hanyar Lafia zuwa Makurɗi.

Ma’auratan, Mista da Misisi Alu Anzaku, an ɗaura aurensu ne a ranar 12 ga Afrilu, 2025.

An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure

Majiyoyi masu kusanci da iyalan ma’auratan sun ce da alama suna cikin lokacin amarci lokacin da wannan mummunan lamari ya faru, wanda ya katse sabuwar rayuwarsu tare.

Har zuwa lokacin da ake haɗa wannan rahoto, ’yan uwa da abokan arziki sun ci gaba da nuna matukar damuwa, saboda har yanzu ba a samu wani labari game da inda amaryar da aka sace take ba, ko kuma halin da take ciki.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ba amsa kiran waya da sakonnin tambayoyin da wakilimmu ya aika mata game da lamarin ba har zuwa lokacin da aka kammala rubuta wannan labarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Amarya Ma aurata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa

An kama shi ne sakamakon wani mummunan al’amari da ya faru kwanan nan, wanda ya yi sanadin mutuwar wani babban bafadan masarautar, John Ikhamate, lamarin da ya tayar da ƙura da kira na ganin an samu adalci.

Gwamna Okpebholo ya tabbatar wa da jama’a cewa gwamnatinsa na da niyyar yaƙar rashin tsaro a faɗin jihar, tare da ɗaukar mataki kan shugabannin al’umma da suka gaza yin abin da ya dace a yankunansu.

Ya kuma buƙaci sarakunan gargajiya da su mara wa gwamnatinsa baya wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin gwiwa da jami’an tsaro.

Gwamnatin jihar ta kuma buƙaci al’ummar Masarautar Uwano da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka yayin da bincike ke gudana kan lamarin kisan.

Haka kuma ta gargaɗi duk wani shugaba da aka samu da hannu a aikata ko ɓoye laifuka zai fuskanci hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  • Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Dabbobi 4 A Wani Hari A Filato
  • Kotu A Kano Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Matashi Da Ya Kashe Ƙanwarsa Da Kishiyar Mahaifiyarsa
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa