Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare Hare Kan Yakuna 4 A Kasar Yamen
Published: 25th, April 2025 GMT
A cikin sabban hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen a jiya Alhamis sun kai hare-hare kan larduna guda 4 .
Tashar talabijin ta Presstva anan Tehran ta nakalto majiyar labarai daga kasar ta Yemen jiragen yakin Amurka suna kai hare-haren a kan kasar kusan ko wani rana.
Amurka dai tace tana kai wadan nan hare-hare kan kasar Yemen ne sai ta dakadar da kaiwa HKI hare-hare don goyon bayan Falasdinawa a Gaza, sannan ta dakatar da kaiwa Jiragen HKI da kuma na Amurka hare-hare a cikin tekun maliya.
Kamfanin dillancin labaran SABA NEWS na kasar Yemen ya nakalto wani jami’an gwamnatin kasar wanda bai son a bayyana sunansa yana cewa jiragen yakin Amurka sun kai hare hare a safiyar yau Jumma’a a tsibirin Kamaran da ke kudancin kasar kusa ba bakin tekn red sea.
Sannan makaman na Amurka sun fada kan yankin Bani Hushaysh da ke daya daga cikin lardunan da suke kusa da San’aa babban birnin kasar.
Labaran sun kara da cewa makaman Amurka sun fada kan garin Hakamal-Haymah da yankin Manakhah duk a kusa da birnin san’aa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi Ya Ce Kasar Sin Za Ta Magance Cin Zarafin Da Amurka Ke Yi Ita Kadai
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da magance cin zarafin da Amurka ke yi ita kadai, ba wai kawai don kare hakki da moriyarta ba, har ma da kiyaye moriyar kasashen duniya. Ya bayyana hakan ne a jiya Jumma’a yayin ganawarsa da takwaransa na kasar Tajikistan Sirojiddin Muhriddin.
Ministocin harkokin wajen kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan da suka shafi harajin kwastam yayin da suka hadu a birnin Almaty domin halartar taron ministocin harkokin wajen kasashen tsakiyar Asiya da kasar Sin karo na shida.
Wang, ya nanata cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da dukkan bangarori domin tabbatar da gudanar da kasuwanci cikin ‘yanci, da nuna adawa da kariyar cinikayya, da kare daidaito da adalci a duniya.
Yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Uzbekistan Bakhtiyor Saidov, duk dai a wannan ranar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashe masu ra’ayi iri daya, wajen kiyaye damawa da kowa da kowa, da kare daidaito da adalci, da kuma nuna adawa da kariyar cinikayya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp