Gwamnatin kasar Amurka ta gargadi kasar Ukraine a dai dai lokacinda ta gabatar da shirin zaman lafiya da kasar Rasha na karshe.

Shirin da shugaban kasar Donal Trump ya bayyana shi ne karshe dai, ya bukaci gwamnatin shugaba Volodimir Zelesky ta amince da yankin Cremea da kuma sauran yankunan hudu wadanda Rasha ta mamaye da karfi shekaru uku da suka gabata su zama mallakin kasar Rasha har’ abada.

Sannan ta amince a daukewa kasar Rasha takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata tun bayan fara yakin. Sannan daga karshe ta amince ba zata shiga kungiyar tsaro ta NATO ba.

Shawara bata yi maganar wani abu banada wadannan hudu ba, duk da cewa Ukraine tana da wasu bukatu a yarjeniyar tsagaita wuta da kuma samar da sulhu mai dorewa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa Moscow ta bukaci a tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu don samun damar tattaunawa amma gwamnatin Kiev ta ki amincewa.

Masana suna ganin wadannan al-amura suna da nauyi ga kasar ta Ukraine, amma kuma bata da zabi tunda Amurka ce ta biya mafi yawan kudaden da Ukraine ta kashe a yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sakataren PDP: Damagum ya amince da matsayar gwamnoni

Muƙaddashin Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa, Ambasada Umar Damagum, ya umarci jami’an jam’iyyar da su yi karɓi Arch. Setonji Koshoedo a matsayin mukaddashin sakataren jam’iyya na ƙasa.

Gwamnonin PDP, a taron da suka yi a Ibadan, Jihar Oyo, sun amince da Koshoedo a matsayin mukaddashin sakatare har sai lokacin da shugabannin shiyyar Kudu maso Gabas za su zaɓi cikakken sakatare wanda Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar zai amince da shi.

Kotun Ƙoli, a hukuncin da ta yanke kan wanda ya cancanci ya riƙe muƙamin tsakanin Sanata Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye, ta ba jam’iyyar ikon yanke shawara kan shugabanninta.

Sai dai a wata takarda da Alhaji Gurama Bawa, jami’in gudanarwa na mukaddashin shugaban jam’iyyar ya fitar, ta ce Setonji Koshoedo, Mataimakin Sakatare na Ƙasa (DNS), yanzu shi ne Mukaddashin Sakatare na Ƙasa na babbar Jam’iyyarmu har sai an sanar da wani abu.

Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci

Takardar ta kuma roƙi ma’aikatan jam’iyyar da su ba sabon mukaddashin sakataren goyon baya wajen gudanar da ayyukansa.

Takardar ta ce: “Dangane da abin da ke sama, duk wasiƙun jam’iyyar ya kamata a tura su ga Hon. (Arch) Setonji Koshoedo.

“An roƙe ku da ku ba shi duk goyon baya da haɗin kai da ys dace a matsayinsa na Mukaddashin Sakatare na Ƙasa na babbar Jam’iyyarmu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yayin Da Ake Fuskantar Daminar Bana: Sabbin Hare-hare Na Barazana Ga Shirin Wadata Kasa Da Abinci
  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • Ficewar Kawu a jam’iyyarmu zai kawo zaman lafiya – Shugaban NNPP na Kano
  • Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Sakataren PDP: Damagum ya amince da matsayar gwamnoni
  • Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa