Hon. Ibrahim ya yi nuni da cewa a karkashin jagorancin Gwamna Abba an samu ci gaba sosai wajen tabbatar da samar da ingantaccen ilimi ga kowa da kowa da kyautata harkar lafiya da sufuri da biyan ma’aikata da ‘yan fansho hakkokinsu ba tare da jinkiri ba.

 

Kwamishinan ya jaddada goyon bayansa ga irin ayyukan raya kasa da Gwamna Abba ke yi, musamman a fannonin ilimi, kiwon lafiya, bunkasa matasa da bunkasa harkar kasuwanci da sufuri a fadin Jiha Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

Bankin Zenith ya kasance a kan gaba tare da samun ribar naira tiriliyan 1.32 kafin a biya haraji, wanda hakan ke nuna karin kashi 67 cikin 100 daga naira biliyan 796 da aka samu a shekarar 2023.

 

Bankin GTCO ya bi sahu, inda ya fitar da ribar kashi 107.8 kafin a fara biyan haraji zuwa naira tiriliyan 1.266, daga naira biliyan 609 na bara.

 

Har ila yau, Access Corp da UBA sun taka rawar gani sosai, inda suka samu ribar naira biliyan 867 da kuma naira biliyan 803.7, wanda ya zarce adadin da suka samu a shekarar 2023 na naira biliyan 729 da kuma naira biliyan 757.6.

 

First HoldCo ya kuma samu ribar kashi 124 cikin 100 na ribar da aka samu, daga naira biliyan 347.9 a shekarar 2023 zuwa naira biliyan 781.9 a shekarar da ta gabata.

 

Masu gudanarwa sun yi amanar cewa juriyar da fannin banki ke nunawa ba wai kawai shaida ce ga daidaitawar cibiyoyin hada-hadar kudi ba har ma da nunin damar da za a samu nan gaba, musamman ga masu saka hannun jari da ke sa ran samun kwanciyar hankali.

 

Ko da yake sun bayar da hujjar cewa, idan aka yi hasashen farashin kudin ruwa zai ragu, kuma nairar za ta kara karfi tare da rage sauyin yanayi, ribar bankunan na iya fuskantar matsin lamba a bana.

 

Duk da haka, kwararrun sun ci gaba da jajircewa kan fannin, tare da lura da cewa bankunan da ke da kakkarfan habakar lamuni da kuma dabarun samun kudin shiga maras riba, musamman wadanda ke yin amfani da ayyukan kasuwanci, da alama za su kasance masu jan hankali ga masu zuba jari.

 

Wani manazarci, Charles Abuede, ya ce ayyukan bankunan Nijeriya a cikin shekara ta 2024 suna ba da manuniya mai kyau ga abin da ke gaba a 2025.

 

Ya ce, akwai hasashen za a samu karin tagomashi sosai a bangarorin a shekarar bana, wanda a cewarsu ayyukan na kyau matuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Kare-Karen Haraji Ba Zai Bunkasa Arzikin Amurka Ba
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC
  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC
  • Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi