Shugaban Amurka ya bayyana cewa: Fira ministan Isra’ila Netanyahu ba zai ja shi zuwa shiga cikin yaki da Iran ba, kuma a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci da shugaban kasar Iran

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya jaddada cewa: Ba za a sanya shi shiga yaki da Iran ba saboda manufofin fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Trump ya kara da cewa a wata hira da ya yi da mujallar Time, a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci ko kuma shugaban kasar Iran.

Duk da imanin da ya yi cewa: Amurka da Iran za su iya cimma yarjejeniya, amma Trump ya sake nanata barazanarsa na cewa idan ba a cimma matsaya ba, to zai bi sahun ‘yan yahayoniyya wajen kai wa Iran hari, domin ganin cewa, Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Trump ya kuma musanta yunkurin cewa zai hana Isra’ila kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kakabawa Kamfanonin Da Suka Hulda Da Iran Bangaren Man Fetur

A dai-dai lokacin da kasashen Amurka da JMI suke ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliya ta Iran gwamnatin Amurka a jiya Laraba ta dorawa kamfanoni da mutanen da suke mu’amala da JMI a bangaren man Fetur takunkuman tattalin arziki. Da dama daga cikin wadannan kamfanoni na kasar China ne.

Jaridar ‘the Nation’ ta Amurka ta ce tun farkon wannan shekarar ne shugaban Trump ta farfado da takurawar tattalin arziki  mafi muni a ka kasar Iran da nufin tilasta mata dawowa teburin tattaunawa ko kuma ta wagaza cibiyoyin Nukliyar kasar.

A halin yanzu dai kasashen biyu zasu ci gaba da tattaunawar ba kai tsaye ba,  karo na hudu a birnin Roma na kasar Italiya a ranar Asabr mai zuwa. Kuma mai yuwa daga karshe su samarda sabuwar yarjeniya a tsakaninsu, kuma akwai yiuwar su kasa yin haka.

Wannan kuma zai faru ne idan Amurka ta bukaci JMI ta daina mu’amala da sinadarin Uranium kwatakwata ko kuma ta shigar da wata bukata wacce Iran ba zata amince ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce Ba Zata Amince Da Barazana Da Kuma Takurawa A Lokaci Guda Da Tattaunawa ba
  • Limamin Jumma’a A Nan Tehran Ya Ce Iran Tana Da Masu Tattaunawa Da Amurka Kwararru
  • Ma’aikatan Da Ba Malamai Ba A Jami’ar Jihar Taraba Sun Fada Yajin Aiki
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka
  • An dage tattaunawa ta hudu da aka shirya gudanarwa tsakanin Iran da Amurka
  • Kamala Harris Ta Zargi Trump Da Haddasa Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi
  • Amurka Ta Kakabawa Kamfanonin Da Suka Hulda Da Iran Bangaren Man Fetur
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Arif: A Shirye Muke Mu Sabunta Sana’o’in Sudan
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya