An kashe Shugaban coci da wata mace a Benuwe
Published: 25th, April 2025 GMT
A wani sabon tashin hankali ya yi sanadiyyar rasa rayukan wani shugaban cocin Roman Katolika da wata mata a ƙauyen Ayua da ke gundumar Mbayer/Yandev a ƙaramar hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Shedun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne a daren ranar Talata, lamarin da ya sa mazauna yankin da ke kewayen yankin Mbagwen da ke ƙaramar hukumar Guma ƙaurace wa gidajensu sakamakon hare-haren da ’yan bindiga ke kaiwa.
Waɗanda aka kashen dai sun haɗa da: David Hur, shugaban shiyyar Cocin Anter Catholic da Misis Lydia Utuu ta ƙauyen Ayua.
Majiyoyi sun yi zargin cewa rikicin ya samo asali ne sakamakon wata arangama tsakanin wani makiyayi da wani mazaunin ƙauyen.
Rahotanni sun ce makiyayin ya yi yunƙurin wanke kansa ne a wata hanyar ruwa ɗaya tilo da al’umma ke da shi bayan ya sha daga ciki. Wani ɗan unguwar ya nuna rashin amincewarsa, wanda hakan ya haifar da rikici inda ake zargin makiyayin ya kai masa farmaki da adda.
“Mutumin ya yi neman agaji don jawo mutanen ƙauyen zuwa wurin, amma hargitsin ya kaure da sauri zuwa wani mummunan yanayi,” kamar yadda wani mazaunin garin ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho.
Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, mazauna yankin sun bar gidajensu da yawa. Har yanzu dai ana zaman ɗar-ɗar, tare da yin kira ga gwamnati da jami’an tsaro su shiga tsakani domin daƙile ci gaba da zubar da jini.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe, CSP Catherine Anene ba ta amsa tambayoyi kan lamarin ba don ƙarin haske a lokacin haɗa wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Makiyayi Mbayer Yandev
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Dabbobi 4 A Wani Hari A Filato
Ya roƙi matasa da su zauna lafiya kuma su riƙa kai rahoton duk wani abu na barazana ga jami’an tsaro, domin nemo mafita game da hare-haren da ke ci gaba da faruwa.
Garba Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da makiyayan shida ke kiwo.
“Da maharan suka fara harbi, ɗaya daga cikin makiyayan da ya tsira ne ya kira ya ba mu labari. Ina samun labarin, na garzaya wani shingen sojoji da ke Latiya, inda na kai rahoto. Daga nan jami’an tsaro tare da ni muka tafi wajen, mun tarar da shanun da tumakin da aka kashe,” in ji shi.
Shugabannin ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da GAFDAN a jihar, Ibrahim Babayo da Garba Abdullahi, sun yi kira ga hukumomin tsaro da su binciki lamarin tare da hukunta waɗanda suka aikata laifin.
Haka kuma sun roƙi mambobinsu da su zauna lafiya kuma ka da su ɗauki doka a hannunsu, su bar hukumomin tsaro su ɗauki mataki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp