Abu Ubaidah: Mun Harbo Sojojin Mamaya 4 Daga Nesa A Beit-Hanun
Published: 26th, April 2025 GMT
Mai Magana da yawun dakarun ‘Kassam” Abu Ubaidah ya sanar da cewa; sun harbo sojojin mamaya 4 ta hanyar wani kwanton bauna da su ka yi musu a Beit-Hanun.
Kakakin dakarun na ” Kassam” ya kuma ce; Har yanzu suna ci gaba da kwamawa da ‘yan mamaya da kuma yi musu kwanton bauna a wurare mabanbanta.”
Abu Ubadah ya kuma jaddada cewa; ‘yan gwgawarmaya su ne ke zabin lokacin da wurin da za su kai wa abokan gaba hari, kuma jaruntarsu tana bayyana daga garin Beit Hanun zuwa Rafah, da hakan yake a a matsayin abin alfahari ta fuskar soja.
A ranar Alhamis din da ta gabata, ‘yan gwgawarmayar sun harbo sojojin HKI 4 daga cikinsu har da masu manyan mukamai, tare da halaka su da kuma jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Gargadin Munanan Sakamakon Da Zai Biyo Bayan Kashe Falasdinawa
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran yayi kashedin kan illar ci gaba da killace Gaza da kuma hare-haren ta’addancin ‘yan mamaya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Ci gaba da rashin hukunta ‘yan sahayoniyya kan kisan gillar da suke yi a zirin Gaza da Gabar yammacin kogin Jordan, da kuma mamayar wasu yankunan kasar Labanon da Siriya yana da matukar barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Juma’a, Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan ci gaba da ayyukan wuce gona da iri da na ta’addancin yahudawan sahayoniyya a Gaza da Lebanon.