Duk da kasancewarta matar aure kuma uwa daga Arewacin Nijeriya, sannan kuma ga karatu tana yi, a lokaci guda, amma hakan bai hana ta samun nasarar zama gwarzuwar ɗalibar da ta kafa sabon tarihin da sai da aka shekara 35 rabon da a samu wani mahaluki da ya kafa irinsa a fannin ilimin shari’a.

A yayin da take karatu, A’isha Widad, mai shekara 24 a duniya, ta fuskanci ƙalubalen da suka danganci haɗa karatu mai zurfi da kuma rayuwar aure — kama daga ɗawainiyar kula da gida zuwa na juna biyu da na jego da kuma shayarwa — amma duk da haka, ta kafa tarihin zama mutum ɗaya tilo da ta kammala digirinta na farko da Daraja na ɗaya (First Class), wanda an shekara 35 rabon da a samu wani mahaluki da ya kai wannan mataki a Tsangayar Koyon Shari’a ta Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).

Karatun aikin shari’a na daga cikin waɗanda ake ganin sun fi wahalar wa, ga shi kuma sai an shafe shekara biyar ake kammala digirinsa. Sannan kuma a je a shekara guda ko fiye da haka, a Makarantar Koyon Aikin Lauya, ya danganci lokacin da mutum ya ci jarabawar kammala makarantar.

A’isha Widad Yahaya, ’ya ga shahararren malamin tarihin nan, Marigayi Farfesa ɗahiru Yahaya, ta zama mutum ta farko da ta kafa tarihin kammala karatu da digiri mai daraja ta ɗaya a fannin aikin Shari’a a Jami’ar BUK, a tsawon shekara 35 da suka shuɗe.

Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi

A cikin wannan tattaunawar da ta yi da Aminiya, gwarzuwar ɗalibar ta bayyana irin ƙalubalen da ta fuskanta da ma wasu abubuwan:

 

Farkon rayuwata

An haife ni ne a ƙaramar Hukumar Ungoggo ta Jihar Kano a ranar 3 ga Yuli, 2001, hakan yana nufin shekaruna 24 da haihuwa a yanzu. Na fara yin makarantar firamare ne a Al-Azhar Kano, sannan na wuce Kwalejin Musa Ilyasu inda na yi karatun sakandare. Daga baya na samu nasarar samun shiga Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) inda na karanci Aikin Lauya.

Goyon bayan da na samu

Da farko ba ni da niyyar yin karatun aikin lauya ko harkar shari’a. Amma a lokacin da aka ba mu zaɓi a makarantar sakandare cewa mu zaɓi ɓangaren kimiyya ko ‘art’, sai da na je gida na nemi shawarar mahaifina, a lokacin yana raye.

Mahaifina, Marigayi Farfesa ɗahiru Yahaya, ya shaida min cewa, idan fannin ilimin kimiyya nake so in karanta, to zai ba ni shawarar bayan na kammala

sakandare na karanci ilmin aikin likita; Idan kuma ‘art’ nake so, to yana shawarta ta da in karanci ɓangaren Shari’a bayan na gama sakandare.

Ba zan iya cewa burin mahaifina ne in zama lauya ba, iyaka dai ya ba ni shawara ne kawai, ni kuma na ɗauki shawarar tasa a lokacin da damar hakan ta samu.

Ƙalubale a matsayin matar aure, uwa kuma ɗaliba

ƙalubale na farko shi ne, ni ba a makwancin ɗalibai da ke cikin makaranta nake ba, don haka a kullun sai na tashi da sassafe a kowace rana tun daga garin Ungoggo da nake zaune zuwa BUK, kuma ka san wajen da nisa sosai.

Haka zalika, karatun tsangayarmu na farawa ne a mafi akasarin lokuta da misalin ƙarfe 8:00 na safe. A gaskiya abin da wahala sosai, amma a haka na ɗaure na jure har na kammala.

Ƙalubale na biyu shi ne lokacin da na yi aure. Na yi aure lokacin da nake a shekara ta huɗu a fannin karatuna wato leɓel four. Yin aurena ya buɗe sabon shafi a rayuwata domin yin aure da zuwa makaranta a lokaci guda ba abu ne mai sauƙi ba ko kadan.

Amma na samu ƙwarin gwiwa da goyon bayan mijina sosai wanda hakan ya taimaka min wajen kaiwa wannan matakin da na kawo a halin yanzu. Haɗa ɗawainiyar aure da ta neman ilmi ko in ce karatu ba abu ne mai sauƙi ba, amma Allah cikin ikonSa, na samu nasarar kawowa zuwa wannan matakin.

Ƙalubale na uku da na fuskanta shi ne lokacin da na haifi jaririna. A gaskiya abu ne mai mutuƙar wahala daidaita harkar karatu, zaman gidan aure da kuma ɗawainiyar raino.

Idan zan bayyana wannan yanayin, nakan ce da mutane, wannan yanayi ne mai ƙayatarwa amma mai cike da ƙalubale.

A wasu lokutan sai nayi tunanin ba zan iya ba, na ji kamar na watsar da karatun na fuskanci aure da shayarwa. Amma Alhamdulillah da dukkan taimakon da na samu daga ’yan uwa da abokan arziki, malamaina da sauran mutane da kuma uwa uba mai gidana haɗe da jajircewata, Allah Ya sa yanzu komai ya zama tarihi.

Ba ni da burin samun ‘First Class’

Ban taɓa tunanin kammala jami’a da ‘First Class’ ba, saboda al’adar da na tarar a makarantarmu cewa abu ne mai wahalar gaske ɗalibi ya kammala da First Class a sashen koyon aikin shari’a. Ni dai na sa a raina zan yi iya bakin ƙoƙarina kawai na kammala karatun.

Amman a lokacin da nake shekarar karatu ta biyu wato ‘Leɓel 2’ a gaskiya na yi mamaki da naga na fito a mataki 5.0.

Tun daga wannan lokacin na ƙara jajircewa tare da taimako da ƙarfafawar da nake samu daga abokaina, iyalina da malamaina, na kai ga matakin samun nasara.

Sirrin nasarata

Kasantuwar samun nasarata na da alaƙa ne da taimakon da na samu a wajen mijina da kuma yadda na jajirce wajen ganin ban bai wa kowa kunya ba. Haka zalika kasancewar mijina malami ne shi ma a wani sashe daban a jami’ar da nake, na amfana da irin ƙwarin gwiwa da kuma shawarwari irin na ƙwararru da ya ringa ba ni.

Ya kuma tabbatar da cewa na samu duk irin taimakon da nake buƙata idan hakan ya taso. Ya kasance a ko dayaushe yana faɗa min cewa “zan iya saboda ya san zan iya din.” Shi mutumin kirki ne kuma ginshiƙi a harkar karatuna.

Taimakon da na ƙara samu shi ne daga ’yan uwana na jini. Kasancewar a cikin ’yan uwana akwai guda biyu wadanda suka kammala karatu a fannin shari’a, hakan ya ba ni damar samun taimako ta ɓangaren karatuna domin sun ƙara min karfin gwiwar in ci gaba da jajircewa.

Haka kuma Shugaban Sashen Shari’a da kuma mai kula da ’yan ajinmu, dukkansu sun taka muhimmiyar rawa wajen tallafa mini da kuma ƙarfafa min gwiwa in ci gaba da ƙoƙari, waɗannan mutane sun taka muhimmiyar rawa a rayuwata.

’Yar baiwa ce — Barista Abba Hikima

Barista Abba Hikima lauya ne mai zaman kansa wanda shi ma ya kammala karatu a fannin shari’a a Jami’ar Bayero, haka zalika lauya ne mai fafutuka a ɓangaren shari’a wanda kuma ya kasance jagora ga A’isha a lokacin ɗalibtarta.

Ya ce, “Na haɗu da A’isha lokacin da suka fito don samun horo na keke-da-keke a fannin shari’a. Ta zo ofishina a matsayin ɗaliba mai neman sanin makamar aiki. Na duba takardunta, sai na fuskanci cewar akwai alamar wannan baiwar Allah za ta bayar da mamaki ƙwarai.

Daga wannan rana muka sanya burin samun ‘First Class’ a fannin shari’a duk da ƙalubalen da take fuskanta a matsayinta na ’ya mace kuma uwa.

A’isha ta ƙara wa sauran mata ƙaimi

Asma’u Aminu Sani, it ace malamar da ke kula da ajin su A’isha a Jami’ar Bayero, kuma tun farkon karatunta a jami’ar ta tsaya mata kai da fata wajen ganin mafarkinta ya tabbata.

A cewarta, “A’isha ta nuna jajircewa da ƙwazo wajen samun nasararta a karatun, duk kuwa da irin tarin ƙalubalen da ta fuskanta.”

Malamar ta ce, “Mutum ne ya taɓa kafa irin wannan tarihin kimanin shekaru 35 da suka shuɗe, kuma a yanzu ma mutum ce ta sake kafa shi.”

Ta bayyana A’isha a matsayin wata gwarzuwa wacce rayuwarta za ta ci gaba da zama abin kwatance ga dukkan mata, la’akari da yadda ta iya tsallake dukkan tarin ƙalubalen nata har ta kai ga gaci.

“A kodayaushe nakan ba ta labarin irin gwagwarmayar da na sha a baya domin na ƙarfafa mata gwiwa a duk lokacin da harkokin karatun suka cukurkuɗe mata da ɗawainiyar iyali da kuma sauran buƙatun rayuwa. Tana da matuƙar sauraon shawarwari sannan tana da saurin fahimta.

“Rayuwarta wata kyakkyawan misali ce wacce ke nuna cewa ta hanyar jajircewa da aiki tuƙuru za a iya cim ma abubuwa da dama. Jajirtacciyar mace ce, kuma ina alfahari da kasancewa a cikin tarihin nasarar rayuwarta,” in ji ta.

 

Daga Ibrahim Musa Giginyu, Aisha Ahmad Manzo da Sa’adatu Shu’aibu, Kano

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaliba karatu Shari a kammala karatu fannin shari a Jami ar Bayero a a Jami ar

এছাড়াও পড়ুন:

An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure

Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi ta sallami ɗaya daga cikin malamanta, Dokta Usman Mohammed Aliyu daga jami’ar bisa zargin neman yin lalata da wata ɗaliba matar aure da ke karatun digiri na biyu.

Idan dai ba a manta ba, Kamila Rufa’i Aliyu, ɗalibar Sashen koyon aikin injiniya ce, a shekarar bara ta roƙi mahukuntan Jami’ar ta hannun tsangayarsu da su binciki lamarin.

Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace

Ɗalibar ta kuma zargi Dakta Aliyu da yi mata barazanar rashin samun nasarar karatunta idan har ta ƙi amincewa da biyan buƙatarsa.

Malamin da ya samu labarin ƙarar da aka shigar da shi, an shigar da ƙarar a gaban kotu a kan zargin ɓata suna a kan wata ɗaliba, tsangayar da Jami’ar.

Amma Jami’ar a cikin Jaridarta (ATBU Herald) ta Afrilu 22, bugu na Vol. 39 lamba ta 5 ta bayyana cewa majalisar gudanarwa ta jami’ar ta kori Dakta Usman Mohammed Aliyu daga aiki a jami’ar.

Jaridar ta ce: “A zamanta na yau da kullun karo na 96 da aka gudanar a ranar Juma’a, 11 ga Afrilu, 2025, Majalisar ta amince da korar Dakta Aliyu bisa laifin neman yin lalata da ɗalibar.”

Rahoton ya ce korar ta biyo bayan wani rahoton da kwamitin ladabtarwa na manyan ma’aikatan ya yi wanda ya same shi da aikata laifin.

“Sanarwar ta ci gaba da cewa korar ta biyo bayan babi na 3, sashi na 1, (o) na sharuɗɗan manyan ma’aikatan jami’ar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Masana’antun Nijeriya Sun Kashe Naira Tiriliyan 1.11 Wajen Samun Wutar Lantarki A 2024 – Rahoto
  • Rashin Wutar Lantarki: Jihohin Kano, Katsina Da Jigawa Na Samun Wutar Awa 2 Ne Kacal A Kullum
  • Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4
  • ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa 
  • Kare-Karen Haraji Ba Zai Bunkasa Arzikin Amurka Ba
  • An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure
  •  Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi