Leadership News Hausa:
2025-04-26@16:17:59 GMT

Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake

Published: 26th, April 2025 GMT

Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake

Wannan dai, wani bangare ne na shirin kara habaka hada-hadar kawance tsakanin kasar da China.

 

Kazalika, hakan na daga cikin yunkurin Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, na jawo masu zuba jari da yawansa ya kai kimanin dala biliyan daya a fannin habaka samar da Sikari a kasar.

 

Bisa tsarin wannan yarjejeniya, kamfanin zai kafa masana’antar Sikari da kuma gonar Rake da za su fara samar da tan 100,000 na Sikari a duk shekara.

 

Kazalika, Hukumar NSDC ita kuma, za ta taimaka wajen samar da duk takardu da kuma sahalewar gwamnati da ake bukata, domin fara aikin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sayyid Fadhlullahi Ya Jaddada Muhimmanci Samar Da Makamai Ciki Har Da Kare Kasa Daga Dan Mamaya

Sayyid Fadlallah ya bayyana cewa: Ana samar da makamai ne domin kare kasa da kuma matsa wa abokan gaba

A cikin hudubar sallar Juma’arsa daga mumbarin masallacin Imamain al-Hassanain (amincin Allah ya tabbata a gare su) da ke Haret Hareik a kudancin birnin Beirut, Sayyid Ali Fadlallah ya yi kira da a dauki dukkan matakai na tursasawa makiya yahudawan sahayoniyya janyewa daga yankin kasar Lebanon da ta mamaye, da daina kai hare-haren wuce gona da iri kullum rana kan yankunan Lebanon, da kuma sakin mutanen da suka kama a matsayin fursunonin yaki.

Malamin ya bukaci dukkanin ‘yan kasar Lebanon, ba tare da la’akari da mazhabobin su ba, ko kungiyoyinsu, ko kuma matsayinsu na siyasa, da su tashi tsaye wajen gudanar da hakkokin da sukarataya a wuyarsu kan kasarsu, da kuma fuskantar wadanda ke yin zagon kasa ga ikon kasa da tsaro, da zaman lafiyarta, da kuma samun hadin kan muryarsu wajen tunkarar wadannan hare-haren da ke barazana ga zaman lafiyar cikin gida da zaman dukkan al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
  • Rasha Ta Fara Aika Isakar Gas Zuwa Kasar  Iran Ta Azarbaijan Don Sayarwa A Kasuwannin Duniya
  • Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
  • Sayyid Fadhlullahi Ya Jaddada Muhimmanci Samar Da Makamai Ciki Har Da Kare Kasa Daga Dan Mamaya
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare Hare Kan Yakuna 4 A Kasar Yamen
  •  Ministan Tsaron Pakistan Ya Yi Wa Pakistan Barazanar Kai Mata Hari Mai  Tsanani
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  •  Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi
  • Arakci: Mun Yi Tattaunawa Mai Kyau Da Mahukuntan Kasar China