Ministan Harkokin Wajen Kasar Siriya Ya Bukaci MDD Ta Dagewa Kasarsa Takunkuman Tattalin Arziki
Published: 26th, April 2025 GMT
Bayan ya sake daga sabowar tutar kasar Siriya a cibiyar MDD da ke birnin NewYork ministan harkokin wajen kasar Siriya Asaad Al-shaibani, ya gabatar da jawabi a gaban kwamitin tsaro na MDD a jiya jumma’a inda ya roki kwamitin ya dagewa kasarsa takunkuman tattalin arziki wadanda aka dorawa gwamnatin da ta shude.
Jaridar Middle eart Eye ta kasar Burtaniya ta nakalto Al-shaibani ya na cewa takunkuman suna hana ruwa guda a cikin al-amura da dama a kasarsa, kuma suna hana kafuwar gwamnatinsa su kamar yadda ya dace.
Ministan ya ce dage takunkuman ya zama wajibi don samun ci gaban kasar don kuma rage matsin lamban da mutanen kasar suke ciki. Kasashen yamma musamman Amurka da tarayyar Turai da kuma MDD sun dorawa gwamnatin tsohon shugaban kasar Bashar al-asada takunkuman tattalin arziki, don bawa yan tawayen da suke taimakawa nasara a yakin basabsan da aka dauki shekaru kimani 14 ana fafatawa a kasar.
Ya zuwa yanzun dai kasashen Burtaniya da tarayyar Turai da kuma Amurka duk sun daukewa kasar wasu takunkuman tattalin arzikin. Amma har yanzun akwai wasu da dama wadanda ba’a dauke ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Trump Ya Bukaci Ukraine Ta Amince Da Tayin Putin Na Bude Tattaunawa A Birnin Istambul
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bukaci shugaban kasar Ukraine ya amince da tayin shugaban Putin na Rasah na sun hadu a birnin Istambul na kasar Turkiya don tattauna yiyuwar tsagaita budewa juna wuta.
Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto shugaban Trump yana fadar haka a jiya Asabar ya kuma bayyana cewa wannan wata dama ce kawo karshen zubar da jinni tsakanin kasashen biyu na fiye da shekaru uku da suka gabata.
Trump ya bayyana haka ne a shafinsa na yanar gizo, ya kuma kara da cewa, haduwar shuwagabannin biyu zai fayyace matsayin yakin, da kuma yiyuwar dakatar da shi nan kusa. Banda haka haduwarsu zai bawa kasar Amurka damar gane matakin da zata dauka nan gaba, haka ma tarayyar turai.
Kafin haka dai a ranar Asabar da ta gabata ce, shugaba Vladimir Putin na kasar Rasha ya bayyana cewwa, Rasha a shirye take ta bude tattaunawa gaba da gaba da kasar Ukraune a birnin Istambul na kasar Turkiyya a ranar 15 ga watan mayun da muke ciki wato ranar Alhamis mai zuwa.