Wace Kungiya Ce Za Ta Lashe Kofin Zakarun Turai?
Published: 26th, April 2025 GMT
Kungiyar kwallon kafa ta PSG – wadda tuni ta lashe gasar League 1 ta Faransa na daya daga cikin kungiyoyin da ake ganin za su lashe gasar Zakarun Turai ta bana saboda karfin da tawagar take da shi sannan kuma kungiyar a gine take hadi da kwararren mai koyarwa, Luis Enrikue, tsohon kociyan Barcelona da Roma da tawagar kasar Spaniya, yana daya daga cikin kwararrun masu horarwa.
Wani shahararren masanin wasanni dan kasar Sifaniya, Guillem Balague na ganin PSG ce za ta lashe gasar. ”Suna da duk wani abu da ake bukata domin lashe kofin, sun iya rike kwallo, a yanzu kungiyar na da karfi, tana da masu kai hari, da na tsakiya haka ma masu tsaron baya”
Ya kara da cewa hanya guda da za a iya doke kungiyar ita ce idan ‘yan wasanta suka tare a baya domin tsare gida. ”In dai suka tsananta tsare gida to sai an cinye su, amma idan za su fito, to komai zai iya faruwa” a cewarsa.
Sai shi ma Phil McNulty, babban marubucin wasanni na BBC na ganin PSG ce za ta yi nasara a gasar. ”Suna da zaratan ‘‘yan wasa masu kai hari, misali Ousmane Dembele da Khbicha Kbaratskhelia da a yanzu ke kan ganiyarsu, ga kuma Desire Doue da Bradley Barcola wadanda matasan ‘yankwallo ne masu hazaka ”, in ji shi.
Inter Milan
Kungiyar kwallon kafa ta Inter Milan, kungiya ce wadda za a iya cewa babu mai kwarinta a kasar Italia domin yanayin yadda take buga wasa da yadda ba ta bari ana zura mata kwallaye a raga abu ne wanda ya kamata a kalla, sannan kuma akwai zakakuran ‘yan wasa da dama da za su taimaka wajen ganin kungiyar ta kai wasan karshe tare kuma da lashe kofin.
Shima babban wakilin sashen wasanni na BBC, Ian Dennis ya ce Zakarun na Italiya na da kwarin gwiwar lashe gasar, saboda yadda kungiyar ke da karfi musammna masu tsaron bayanta. Ya ce ”Sun fi kowace kungiya da ta rage a gasar karfin tsaron baya, kawo yanzu babu mai tsaron ragar da ya kai Yann Sommer, hana kwallo shiga raga a wasannin gasar ta bana’.
Ya kuma ce ta bangaren masu kai hari ma, kungiyar na da maciya kwallo, musamman Lautaro Martinez da a yanzu ke kan ganiyar zura kwallaye. Sannan wannan ne karo na biyu a kaka uku da kungiyar ke kai matakin wasan kusa da na karshe. Kuma kungiyar – da ke jan ragamar teburin Gasar Serie A – za ta hadu ne da Barcelona a wasan na kusa da karshe.
Arsenal
Kamar yadda kowa ya sani kungiyar Arsenal ce ta fitar da Real Madrid daga gasar a matakin kusa da na kusa da na karshe bayan doke ta 5-1 gida da waje. Wakilin sashen wasanni na BBC, Aled Howell na ganin kungiyar ce za ta lashe gasar. ”Duk da matsalolin da kungiyar ta fuskanta a bana, amma ta iya kai wa wannan mataki a gasar, ai kasan sun shirya wa gasar”, in ji shi.
”Ta fannin tsaron gida, kungiyar na da karfi sosai, haka idan ka duba ‘yan wasan gabanta hadakar Saka da Martinelli da Odegaard za su iya doke duk wata kungiya da suka ci karo da ita.
Kungiyar ta Mikel Arteta, wadda ke matsayi na biyu a teburin Gasar Premier ba ta taba lashe gasar ba a tarihi kuma ‘yan wasan kungiyar irinsu William Saliba da Bukayo Saka da Martin Ordegaard sun bayyana cewa suna son su rubuta sabon tarihi a kungiyar saboda haka za su yi iya yin su domin ganin cewa sun dauki gasar a karon farko a tarihin kungiyar.
Barcelona
Ita kungiyar kwallon kafa ta Barcelona kungiya ce wadda a yanzu babu kungiyar mai sharafinta kuma ita ce ta fitar da Borussia Dortmund daga gasar. Babban wakilin sashen wasanni na BBC, Simon Stone ya ce yana ganin kungiyar ta Sifaniya ce za ta lashe gasar, saboda yadda take kara farfadowa a baya-bayan nan. ”A yanzu kungiyar ta kara karfi musamman bayanta da tsakiya da masu kai hari”, in ji Simon Stone.
Kungiyar, wadda ke matsayi na daya a gasar La Liga na da zaratan matasan ‘yan wasa da ke haskakawa a fagen kwallon kafa da suka hada da Lamine Yamal da Cubersi da Balde da Fermin da Gabi da sauransu. Sanann rabon da kungiyar ta lashe gasar tun 2015 lokacin da take da zaratan ‘yanwasa irin su Lionel Messi da Luis Suares da kuma dan wasa Neymar na Brazil.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: ta lashe gasar wasanni na BBC masu kai hari kwallon kafa kungiyar ta da kungiyar Kungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu
A wannan makon Aminiya ta samu tattaunawa da shahararren jarumi a masana’antar fina-finan Hausa ta Kannyood, Malam Inuwa Ilyasu, wanda ya shafe sama da shekara 40 yana harkar wasan kwaikwayo. Ga yadda tattaunawar ta kasance:
Gabatar da kanka?
To da farko dai sunana Inuwa Ilyasu.
Yaushe ka fara harkar fim?
Gaskiya dai kusan da ni aka fara yin fim kuma lokacin da muka fara yi, mun fara da yin tunanin ya za mu yi saboda kafin nan ai akwai wasan daɓe da muka fara yi.
A wancan lokaci muna faɗakarwa ta wasan kwaikwayo kusan tun wajejen 1970. Daga nan muka fara tunanin ta yaya za mu yi ƙoƙarin mu ma mu fara yin irin namu.
Yawancin fina-finanka kana fitowa ne a matsayin malami, kana faɗakarwa ko bayar da shawara a addinance. Wannan matsayin kai kake zaɓa ko kuwa masu shirya fim ne suke ba ka?
A’a ba ni na zaɓar wa kaina ba.
Idan na fahimce ka, an duba cancanta da kuma wanda aka gani zai iya bayar da abin da ake so ake ɗora ka a kai?
Yauwa, ana yin sa’a ce dai za ni ce ta tarar da mu je, domin ni daman dalilina na yin wasan kwaikwayo shi ne, saboda in samu in cusa aƙida ta addinin Musulunci da tarbiyartarwarsa da kuma cusa al’adarmu da ɗabi’unmu ga matasa masu tasowa. Misali, ai ka ga irin yadda wasu masu fim ɗin Indiya suke cin karensu babu babbaka.
Daga lokacin da ka fara wasan daɓe zuwa yadda ka juya zua yin fim, shin kana ga saƙonnin da kake son isar wa jama’a suna tasiri wajen faɗakarwa ?
Alhamdulillahi, ana samun nasara Insha Allahu, saboda mutane da yawa in na haɗu da su ko kuma ma wasu su ne za su neme ni, su yi yabo saboda Allah Ya sa sun ci karo da wata faɗakarwa da na yi a wani shirin da ta yi tasiri matuƙar gaske ga rayuwarsu.
Ka shafe sama da shekara 40 a sana’ar harkar fim, ko kai ma ka fara tunanin kafa wani kamfani da idan ka yi fim za ka riƙa ɗorawa a manhajar Youtube kamar yadda wasunku ke yi halin yanzu?
To ni irin wannan ba ya cikin tunanina. Kamar yadda na gaya maka a baya, mun fara yi ne da manufa, kuma muna yi ne domin faɗakarwa ga jama’a a ƙarƙashin ƙungiya da na faɗa mai suna “Dabo”. Haka kuma mun samu nasara, domin wasu daga cikin waɗanda suke a Kannywood ɗin cewa suke yi daga kallon fim ɗin da muke yi, suka koya. Wasu kuma daga irin faɗakarwar da ake yi a fim ta ba su sha’awa har su ma suka shigo matsayin masu yin fim. Wani kuma zai ce shi fim ya kalla, ya sa masa soyayyar abin a zuciyarsa, Alhamdulillahi an samu ci gaba sosai da nasara.
Kamar ta wace gaɓa nasarorin da aka samu?
Gaɓoɓin da dama, saboda za ka samu wasannin da muka yi, wasu suka kalla za su ɗauki darasin rayuwa, sannan muna harkar arziki da jama’a, ana ta nuna mana soyayya ba wata matsala. Sannan idan ma suna muke so mu samu, mun samu. Kai wasu ma na raɓe da mu, sun samu sannan akwai da dama da suke son su samu dama kamar yadda muka samu, amma ba su samu ba.
Wato dai fim ɗin duk da ka fito rawar da kake takawa da aka ba ka ana amfana da ita a kan duk abin da ka faɗakar ko ka a addinance ko a al’adance?
Eh, an samu ci-gaba sosai kuma Alhamdulillahi.
Ya kake kallon ƙalubalen da ake samu a tsakanin masu harkar fim?
Ban fahimce ka ba.
Irin ’yan matsaloli da ka taso tsakanin mawaƙa ko masu yin fim na baya-bayan nan da ake zargin su da wuce gona da iri?
Irin waɗannan abubuwan gaskiya muna ta yaƙin su a matsayinmu na dattawa. Amma ka san ɗan-adam sai da hikima.
Wace shawara kake da ita ga Masana’antar Kannywood da kuma masu nufin nan gaba su shigo ta, lura da cewa yanzu ka zama uba a cikinta tun daga kan hukuma da kuma jarumai?
Eh to akwai buƙatar sake duba inda hukuma za ta shigo ta gyara a cikin harkar, domin muna magana ne a kan addini da tarbiyya, musamman ta Musulmi. Ya kamata a ce gwamnati da ta kafa wannan hukuma ta tallafi to kuma ta duba hanyar da za ta tallafa wa wannan harkar saboda harkar fim tana bayar da dama ga matasa ta samun sana’a. Haka kuma tana hana zaman kashe wando. Sannan kuma ana amfani da fim wajen kawar da wasu miyagun abubuwa da suke faruwa a cikin al’umma, ta yadda ba sai an fito, ana kokawa ko kama mutane ba don yin gyaran. Saboda mu ƙalubale gare mu, mu tabbatar masu kallo za su gamsu da abin da muke yi kuma su faɗaka.
Ban sani ba ko akwai wani saƙo da kake son ka isar?
Saƙona shi ne, kowa lallai yana da buƙatar ya sanya hannu wajen tallafa wa wannan harka ta fim, saboda ta shafe shi a abin da ya shafi addininsa da al’adarsa. Don haka ya kamata kowa ya duba ta ina zai taimaka yadda za ta inganta, ta dace da waɗannan muhimman abubuwa.