Leadership News Hausa:
2025-04-26@21:06:58 GMT

An Gano Naira Miliyan 27.8 Da Suke Zirarewa A Albashin Kano

Published: 26th, April 2025 GMT

An Gano Naira Miliyan 27.8 Da Suke Zirarewa A Albashin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta gano matsaloli a cikin tsarin albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi, inda aka gano ma’aikata 247 da suka yi ritaya ko kuma sun mutu, amma suna ci gaba da karɓar albashi.

Wannan bayani ya fito ne daga cikin wata sanarwa da mataimakin shugaban ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Musa Muhammad, ya fitar.

A cewar sanarwar, wannan bincike ya gudana ne a yayin da ake gudanar da aikin tantancewa domin gyara tsarin albashin ma’aikatan gwamnati a jihar.

Har Yanzu Da Akwai Jihohin Da Malaman Makaranta Ke Karbar Albashin Naira 18,000 NLC Ta Yi Zanga-Zanga A Ofishin Wike, Ta Nemi A Biya Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi Albashin N70,000

Sanarwar ta bayyana cewa, duk da cewa waɗannan ma’aikatan sun yi ritaya ko kuma sun mutu, sun kasance suna cikin jerin sunayen ma’aikatan da ke karɓar albashi, wanda hakan ya kai ga biyan kuɗi na ƙarya har Naira miliyan 27,824,395.40 a watan Maris na shekarar 2025 kawai.

Gwamnatin Kano ta tabbatar da cewa an dawo da wannan kuɗi zuwa asusun ƙananan hukumomi, kuma za a ci gaba da bincike don gano duk wanda ya yi wannan zamba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Salary

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa

Ma’aikatar yada labarai ta jihar Kano tare da hadin gwiwar hukumar kula da gidajen Radiyo da Talabijin ta kasa NBC sun shirya taron yini biyu ga masu fafutukar siyasa da masu sharhi kan harkokin yada labarai.

 

 

 

Taron na da nufin tsaftace harkar siyasa da inganta fahimtar juna tsakanin ‘yan siyasa a jihar.

 

An zabo mahalarta taron ne daga jam’iyyun siyasa daban-daban da gidajen rediyo a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

 

A nasa jawabin, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Waiya, ya bayyana cewa, a karshen taron, mahalarta taron za su fahimci ladubban da suka shafi harkokin siyasa.

 

Ya yi Allah wadai da karuwar kararrakin batanci da sunan siyasa, yana mai cewa masu fafutuka na siyasa, masu sharhi kan harkokin yada labarai da masu gabatar da shirye-shiryen siyasa na bukatar ilimin kan kyawawan ayyuka bisa al’adu da addini.

 

Kwamared Waiya ya nanata kudirin gwamnatin jihar na hada hannu da masu ruwa da tsaki domin ciyar da Kano gaba da kuma baiwa ‘yan kasa damar cin moriyar dimokradiyya.

 

“Ba mu zo nan don shawo kan kowa ya canza sheka zuwa wata jam’iyya ba amma don tsaftace tsarin”

 

Shima da yake nasa jawabin, kodinetan NBC na jihar Malam Adamu Salisu ya bayyana cewa taron bitar ya yi daidai da aikin hukumar, don haka akwai bukatar hada hannu da masu ruwa da tsaki domin cimma manufofin da ake bukata.

 

Ya yabawa ma’aikatar yada labarai kan wannan shiri, sannan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su bada gudunmawar ta hanyar samar da zaman lafiya.

 

Ya yi nuni da cewa taron ya yi daidai da aikin hukumar NBC.

 

Ko’odinetan jihar ya bayyana cewa masu fafutuka, masu sharhi kan harkokin yada labarai, da masu gabatar da shirye-shirye na da muhimmiyar rawa da za su taka a fagen siyasar Kano.

 

Da yake gabatar da kasida kan inganta magana mai kyau da kuma nisantar kalaman batanci a kafafen yada labarai ta mahangar Musulunci, babban limamin masallacin Al-furqan, Sheikh Bashir Aliyu Umar, ya bayyana wasu abubuwa guda uku na yada bayanai bisa koyarwar addinin Musulunci, wadanda suka hada da gaskiya, daidaito da kuma sanin yakamata.

 

Shugaban masu fafutukar siyasar jihar Kano, wanda aka fi sani da Gauta Club, Alhaji Hamius Danwawu Fagge, ya bayyana horon a matsayin wanda ya dace.

 

Ya yi alkawarin cewa mahalarta taron za su yi amfani da ilimin da aka samu wajen ci gaban Kano da Najeriya baki daya.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji
  • Gwamnatin Kano Ta Gano  An Biya Wasu Ma’aikatan Bogi Naira Miliyoyi
  • ‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Rashin Wutar Lantarki: Jihohin Kano, Katsina Da Jigawa Na Samun Wutar Awa 2 Ne Kacal A Kullum
  • Kudaden Da Ke Hannun Mutane Sun Ragu Zuwa Naira Tiriliyan 5 – Rahoto
  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB
  • **Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa