Leadership News Hausa:
2025-04-26@22:26:54 GMT

Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari

Published: 26th, April 2025 GMT

Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari

Manomin da zai shuka Irin noman Kanumfari, ana bukatar ya sa hakuri, idan har kana bai wa Bishiyarsa kulawar da ta dace, za ta iya shafe tsawon shekara 100 ko sama da haka.

Ana bukatar wanda zai shuka shi, ya tabbatar ya shuka Irin noman a kasar noma mai inganci, sannan kuma yana daukar dogon lokaci kafin ya kammala girma.

 

3. Ba Shi Kulawar Da Ta Kamata:

Ana iya shuka Irin noman Kanumfari a gida, kuma zai iya yin girma; amma ya fi bukatar yanayin da yake da zafi, haka nan ko da an shuka shi a yanayin da ya dace, yana kai wa tsawon shekara bakwai kafin ya kammala girma, kazalika, ana bukatar wanda ya shuka Irin noman, ya tabbatar da amfanin na samun hasken rana a kullum, har Ila yau, iska mai karfi na yi wa Bishiyarsa illa, musamman a lokacin da take tasowa.

 

4. Ba a son wanda zai shuka Irin nomansa, ya shuka wanda ya bushe, domin matukar aka bar Irin ya bushe, ba zai taba girma ba.

 

5. Ba a son wanda zai noma shi, ya bar Irin a cikin rana, ana bukatar ya samar masa wajen da ya fi da cewa tare da yi masa ban-ruwa akai-akwai, haka nan, ana so a bar Irin ya girma har zuwa wata shida, bayan an shuka shi kafin a canza masa wajen da za a sake shuka shi, haka yawan yi masa ban-ruwa na iya jawo mutuwar Irin da aka shuka shi.

 

6. Ana son Irin nomansa da aka shuka, akalla ya kai daga wata 18 zuwa wata 24, kafin a canza masa wani wajen, haka Irin nomansa na girma ne a hankali, amma ana bukatar Irin ya kasance ya yi karfi sosai, don ya samu sukunin dorewarsa, musamman idan an shuka Irin a fili.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ana bukatar

এছাড়াও পড়ুন:

An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna

An sako limamin cocin Katolika, Rabaran Fada Ibrahim Amos wanda ’yan bindiga suka sace a ranar Alhamis da rana a Kurmin Risga da ke Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna.

Fada Amos, wanda ke aiki a Cocin St. Gerald Ƙuasi Parish ya dawo gida lafiya lau ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 2 na tsakar dare, kwana ɗaya bayan sace shi.

An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe

Bayani kan sakin nasa na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Shugaban Cocin Diocese na Kafanchan, Rabaran Fada, Dakta Jacob Shanet ya fitar, inda ya gode wa Allah tare da nuna godiya ga al’umma bisa addu’o’i da goyon baya da suka bayar a lokacin da lamarin ya faru.

Fada Shanet ya jinjina wa ƙoƙarin ƙungiyoyin tsaro na gari, ’yan sanda da jami’an DSS da suka ba da gudunmawa a lokacin da aka sace limamin.

Yankin Kudancin Kaduna na daga cikin wuraren da rikice-rikice da garkuwa da mutane suka yawaita.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’
  • A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi
  • ’Yan kasuwar da suka ɓoye kayan abinci na tafka asara
  • Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake
  • An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna
  • Sama Da Mutane Miliyan 11 Ne Ke Fama Da Ciwon Suga A Najeriya – Farfesa Zubairu Ilyasu
  • Jigawa Za Noma Rabin Shinkafa Da Ake Amfani Da Ita A Nigeria Nan Da 2030
  • ICC ta ki amincewa da bukatar Isra’ila na soke sammacin kama Netanyahu
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe